chapter 24

571 83 13
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

🤍💚🤍
    *ƘARAMAR BAZAWARA*
           💚🤍💚

    _(Cigaban matar kulle)_

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

TELEGRAM: https://t.me/joinchat/VOW8-BwH_DjWH1YfVcFONA

WATTPAD: https://my.w.tt/4ZfEeBpVecb
OR
@ayeeshatmuhd

         *BY UMMU NAJMA*

*DEDICATED TO, MAI DAMBU*
  And *AISHA ALTO*

24🧝🏻‍♀️
Shiru mama tayi tana nazari, Sulaiman kuwa yana mararin jin amsarta don ya samu ya maida saudat gidan Hajiyar shi da zama kafin kuma yazo yin mai gaba ɗayan,
Ji yake yi kaman ma ya yanke hukunci ba tare da izinin ta ba, kuma hanyar da yabi shine kaɗai wanda zai kaishi ga nasara cikin sauƙi,

"Ai alhaji sulaimanu da baka daku kanka kazo da kanka a kan wannan ƙaramin al'amari ba, babu wanda yaƙi ilimi kuma babu wanda yaƙi ci gaba, a cikin dubban mutanen da kuka tsallake kuka zo kanmu da alkhairi babu abinda zamu ce muku sai Allah ya saka da alkhairi ya ƙara arziƙi idan ita Saudat ɗin tazo mukayi magana da ita ta amince tana son sauya makaranta tayi a wanda kuka sama mata falillahil hamd"

Saidai ta faɗi hakan ne ba don ta yarda kai tsaye ba al'amarin ya ɗaure mata kai, ta yaya akayi Sulaiman ya san Saudat a gidan khamis take zaune? Kuma mai yasa zai bada muhimmanci a kan karatun ta? Ko taje ta buɗe musu sirrin rayuwar ta ne da ita da Khamis suka haramta mata sanar dashi ma kowa suka ji suka tausaya mata?

"To Shikkenan mama ni zan koma bakin aiki duk yanda kuka yi da ita sai ku sanar dani" ya faɗa tare da ajiye musu card ɗinshi yayi mata alkhairi sosai da sauran mutanen gidan kafin ya tafi zuciyar shi cike da takaici wai yanke ƙaramin hukunci ne sai an tambayi ƴar wannan yarinyar ra'ayin ta,

A ganin shi duk abinda ake so tayi ko aka ga ya dace da ita umarni kawai za'a bata ko bata so inya so daga baya zata iya sabawa har taso abin,

******

"Saudat kibi a hankali dan Allah kada ki kai kanki wurin da Allah bai kaiki ba, kin sanar dani waye Zayyad kin ɓoye min abinda kika ce yana damun shi bansan ko menene ba, amman ina so ki sani shi son zuciya ke jawo ɓacin ta, bance idan kina da hali kada ki taimaka mishi ya samu lafiya ba saboda na san irin baiwan da Allah ya miki da familyn ki ma gaba ɗaya,

Amman wa'innan hawayen, da damuwa da kuma canjin yanayi daga gare ki yana nufin wani abu ne daban, kada ki bari zuciyar ki ta saka ki son abinda kika san ba zaki samu ba, zaki iya kuka da nadaman hakan daga baya"

Kallon ta kawai naci gaba dayi a raunane, aunty Yusrah ta nuna damuwa sosai a kaina amman lokaci ya riga ya ƙure, na daɗe da kamuwa da ciwon son Zayyad saidai ko a yanzu daman ban saka ma raina zan iya zama tashi ba kasancewar shi saurayi nikuma BAZAWARA bamu ma dace da juna ba kwata_kwata,

"Ki bar wankin zan ƙarasa, kije kisha magani ki kwanta ki huta nasan bakiyi barci sosai jiya ba"

Shiga ɗaki nayi dan ina ɓukatar hutun kam, na ɓalli paracetamol guda biyu nasha sannan na hau gado na kwanta daidai lokacin da waya na ya fara niman agaji, na san ma mutanen Rumaisa ne suke niman ta na ɗago wayan da nufin amsawa sunan da tayi saving numbern shi a kan layin ya bayyana "bro Zayd"

Taɓe baki nayi ashe Ruma ma ina ganin ta Sallah_sallah ta iya wulaƙanci na ƙin ƙarawa, saurayin nata da bata so ne shine harda saving sunan shi da zagi wai 'b***'uba Zayd' shine ta gajarce shi da bro dan kar a gane ko darajan irin sunan yayan ta da yake dashi ba zata ɗaga mishi ƙafa ba don sitifid ma wani lokaci nakan ji suna kiran shi yaa Zayd,

ƘARAMAR BAZAWARA (Completed)✅Where stories live. Discover now