SHAFI NA BIYU

1.3K 118 3
                                    

  *TSINTAR AYA*     FREE BOOK.

*BILLY GALADANCHI*

*Sak'on gaisuwa zuwaga Babbar Antyna, mace me karamci kuma me girmama, babba da yaro, Alkhairin Allah yakai miki a duk inda kike  Anty mejidda musa*

*Makaranta Littafin tsintar Aya nagode da rububin son dakuka nuna masa tun a shafin farko, Allah yabar k'auna.*

*SHAFI NA BIYU*

Dariya ya kwashe da ita sanda ta shigo motar jikinta yana b'ari, sanda ya fita a gidan ya saisaita kan motar sosai akan titi sannan ya waigo ya kalleta yana wani kashe ido

"Tsuntsu daga sama gashashe, wato lallai 'yar sha bakida hankali, tsammani kike wai Baba zata tab'a yadda da zancenki,kokuma kina tsammanin kamar akwai abinda ze tab'a hanani cimma burina akanki, wlh sekin gane kurenki a hannuna" Batace masa komai ba banda kukan datake kanta asaman cinyoyinta.Batayi tsammanin cewa zekaita garin nasu ba, amma ga mamakinta setaga ya d'auki hanyar garin nasu se faman wak'e wak'en sa yakeyi tamkar wanda akawa bushara da gidan aljanna!

     Harsuka isa be kuma koda kallon inda take ba, gidan nasu babban gidane sosai me yalwar shiguhu kala kala, kana kuma ko wane b'angaren bayan ka wuce shiguhun runface ta bunu da kuma d'akuna wasu ginin laka wasu kuma bukka ce, tsarin gidan kana ganinsa zaka shaida cewar irin gidan daya had'a dukka kowa da kowa ne, ma'ana Extended family.... Tun a soro na k'arshe Bilal yake rafka sallama har ya bazama cikin gidan, harya cire rai da za'a amsa masa sekuma kaman daga sama ya soma ganin mutane tamkar ana yayyafin su suna fitowa, Atare d'aukacin mutanen wurin suka had'a baki wurin ambatar 'yar shara! wanda hakan ba k'aramin k'ara rikitar da ita yayi ba cikin tsananin firgici take kallon kowa idan ta ya sauka akan Baba jere daya tsatsareta da ido tamkar ze cinyeta d'anya. Bilal gaggaisawa yayi da mazan ta hanyar musabaha sannan yace

"Hajiya Barira ce tamun umarni akan in dawo da 'Yar shara gida, tace in sanar daku kuyi hak'uri da k'in zuwan datayi da kanta ta dawo da ita, tanajin kunyar kune ta kasa rik'eta kamar yanda tayi alk'awari, tace hakan ya biyo bayan cikin shegen dake jikin 'Yar shara ne harna tsawo wata biyu, bazata iya abun kunya ba ita kam, sabida haka na dawo da ita tushiyar ta" Tas wurin ya d'auki salati yayinda lokaci d'aya duniyar ta soma juyawa da 'yar shara tana shawagi da ita, wannan wane mummunan k'azafi ne Bilal yake shirin manna mata, sama sama tajiyo muryar Baba jere yana cewa

"Kayi tafiyar ka Bilal, zamu mata hukuncin daya dace da ita" Haka.ta ruk'unk'une wuri d'aya tana gunjin kuka amma sam ta kasa magana har Bilal ya juya sekuma ya dawo kusa da ita ya sunkuya ya ajiye mata wata leda, ga kati nan ajiki lambar wayana, idan azaba tayi azaba kika yanke hukuncin bani kanki seki nemeni a waya kud'ine acikin wannan biredin sekiyita tattalinsa dan nasan kwana bazaki k'ara agarin nan ba zasu koraki" Batace masa komai ba, babu kuma wanda yaji maganar dasuke se ita kad'ai sabida yanda yazo daf da ita yana magana k'asa k'asa...... Haka ya tafi banda kuka babu abinda 'Yar shara takeyi.Kallon tsana Baba jere yabita dashi sannan yace

"'Yar k'wai bani kayan wuta da alamar k'ira" Inna suwai ce tayi azamar kallon sa, murya yana rawa tace

"Jere me zakayi? kallon ta shima yayi

"Bakiji tayi shege ba, yanda nayi da ubanta haka itama zan mata" Idanta ne ya kawo ruwa babu musu ko gaddama a atsakanin su, babu wanda yake ja da hukuncin jere shine me garin garin gaba d'aya kuma biyayya agaresa batada hijabi awurin su dole sesunyi jikinta yana karkarwa ta zube akan gwiwowinta

"Jere ka dubi girman Allah ka sassauta mata, karka manta azabar k'irane yayi sanadin Djoro, kabar 'Yar shara itakam ita kad'ai ne a tsatson Djoro dazan kalla inji sanyi" Wani kallo ta wurga mata yanzu a hautsine

"Bana buk'atar tsatson Djoro a zuri'a ta, Yanda Allah ya kashe Djoro Allah ya kashe D'iyatai daya bari, Idan zan mata k'ira har a tafukan hannayenta zan manna mata sabida azaban wutan yajewa d'an shegen dake shikinta shima ya mutu atare da ita" Kuka ta saka da iyakacin k'arfin ta ruga ta rungume 'yar shara, zuwa lokacin da aka kawo kayan k'ira aka hura huta aka soma d'o'd'in k'arfen iyakacin gigicewa Hafsat ta gigice, batasan me ma'anar hakan ba, amma menene ya kashe mahaifinta ance rashin lafiya yayi, itama ciwon zasu zasu saka mata kome? k'aramar akwatinta ta janyo ta cura wayarta aciki sannan a hankali ta ware biredin nan ta zaro kudinta ta cura a rigar mamanta tanabin kowa da kallo, katin da lambar wayar Bilal yake aciki ma sanda ta d'auka ta adana ajikinta se zare ido take, batasan me za'a mata ba amma tabbas tasan akwai alamun zata dauki yar mitsitsiyar akwatinta ta kwasa aguje inhar ya kasance azabace! Lokacin da k'arfen yayi azabar zafi se wasu maza tagani datakeda yak'inin yan uwanta ne sukazo suka daddafeta tun a nan ta soma ihu mik'ar da k'afarta akayi aka dafe Jere ya daddage ya manna mata k'arfen a tsakiyar tafin k'afarta!!! Wata uwar k'ara data k'walla tsabar azaba seda ta saki fitsari a wando ba shiri, haka ya mata tambari biyu a kowace k'afa zuwa wannan lokacin ta suma batasan inda kanta yake ba, k'ara dafa k'arafan yake yana ik'irarin manna mata a hannu Inna suwai ta rungumeshi tana kuka akan yabar ta a haka, kallon ta yayi yana yamutsa fuska

TSINTAR AYAWhere stories live. Discover now