SHAFI NA UKU

1K 163 3
                                    

*TSINTAR AYA* FREE BOOK

*BILLY GALADANCHI*

*SHAFI NA UKU*

Sumar kansa ya shafa zuwa k'eya cikin tsananin damuwa da fad'uwar gaba mara misaltuwa, mekenan ya faru wa 'yar mutane? yaya zeyi da ita a yanzu? wannan laifin sane ko me? mesa dacen datake tafiya acikin dare tana d'ingishi be tsaya yaji inda zataje ba? menene amfanin zuwansa yanzu? ina ze kaita? Asibiti? they will surely ask of police report ta ina ze fara? besan komai ba, acikin dare yaganta akan ttii anyi raping nata sai kuma me? shi daga ina yake? iska me zafi ya furzar daga cikin bakin sa sannan ya juya ya kuma kallon ta. Wayarsa ya janyo ya kira Muhseen be d'aukaba dama baze d'auka d'inka ba dan yasan baze masa magana ba, dan haka ya masa txt na wurin daze sameshi yanzu amma shiru shiru babu alamun dawowar sako har zuwa mintuna goma,yanada yak'inin cewar tabbas Muhseen bacci yake. k'ara mayarda dubanshi yayi zuwa ga yarinyar k'ok'arin d'aura zaninta take daga kwancen, sanan kuma seja baya take dashi, ganin yana nufota ya tilasta mata mik'ewa da k'yar tana kuka tare da motsa labb'anta sedai sam baya jin metake cewa, gyaran zaman zanin take kokarin yi amma ina se jiri ya d'ebeta ta tafi luuu zata fad'i a sume, da hanzari yayi azamar rik'ota sannan ya zube akan gwaiwowinsa d'auke da ita, kallon fuskarta yake tabbas suma tayi, lallai abun yafi k'arfin tunanin sa, be b'atawa kansa lokaci ba ya zurata a mota ya finciki motar se gida, nanma kwasarta yayi hannu bibbiyu zuwa b'angaren sa yanzu ma aguje kamar kullum, sedai wannan karon kana gani kasan a uzurcen gaske yake, be had'u da kowa ba se mutanen dayake da tabbacin idansu biyu wato munafukan fada, ya tabbatar munafukan fada idansu yanzu yake bude ma, be wani damuba ya haura samansa da ita.

Yafi minti 30 yana tunanin abinda zeyi da yarinyar har lokacin idanshi be kaishi akan tafukan k'afarta, daga bisani sai ya mik'e ya debo ruwan sanyi ya soma kokarin dawo sa ita hayyacin ta ta farka amma ga alama she's unconcious dafe kanshi yayi ya kalli lokaci k'arfe hud'u saura yan mintuna, yaya zeyi? Family Dr. nasu yawa message akan by 6 ya kasance a b'angaren sa akwai patient daze duba masa sannan ya koma yaci gaba da aikin kallon ta har zuwa sanda yaji ana kiran sallan asubah wannan ne ya tilasta masa mik'ewa ya d'auro alwala ya fita masallaci!

Bayan idar da sallan yajima sosai yana lazimi bayan yayi azkhar d'insa da komai sannan ya mik'e tsaye yana duba message d'in likitan dake tabbatar masa da cewar baya k'asar gaba d'aya, k'aramin tsaki yaja ya fito sekuma yayi karo da Muhseen dake jiransa a k'ofar masallacin dakuwa ko ba'a gaya masa ba ya tabbatar cewar yana masallacin a irin wannan lokacin musabaha sukayi sannan yabi bayanshi zuwa ciki danya tabbatar baze samu amsar komai ba se'a rubuce. Turus Suka tsaya suka kalli jama'ar dake wurin motar Mood ciki kuwa hadda me martaba, k'arasawa yayi shida Muhseen atake muhseen ya zube ya gayar da Me martaba, shikuwa yayi tsaye tamkar an dasashi a wurin ya kafe Me martaba da ido yana jira yaji mezaice wanne kalan labari zezo dashi yau kuma da sanyin safiyar nan, shid'inma shi yake kallo cikeda takaici

"Munaso musan wannan jinin daya fito daga motarka daga ina yake? menene asalin abinda ya faru? munyi tsammanin cewar ai rauni kaji sekaga fess dakai, amma wannan layin jinin dayayita d'iga har zuwa k'ofar d'akinka yake tun daga mota, gashi ana iya hangowa daga motar daka hau jiya aciki akwai jini a sit d'in baya dukda bame yawa bane ba, meke faruwa?" Har wannan lokacin be motsa ba ya daddage ya kafeshi da ido bayako k'iftawa, Muhseen ne ya rik'o hannunsa suka kalli juna yamai magana irinta kurame ma'ana sighn Language yace dashi

"Bro mana meke faruwa? karka bari wani mugun abu ya faru dakai a wannan safiyar, bannason kafiyar nan kakuma sani please talk" Nan d'inma kallon Muhseen kawai yake seda ya gama k'arewa Muhseen kallo sannan yayi amfani da sighn language(Yaren kurame) yace dashi

"Duk Munafukai ne fa! bakaga suna kallona ba, sunsai komai kome zanyi konace bazan wanke kaina ba sun gama shirya komai tsaf so i will not say a word" Dafe kai Muhseen yayi, Me martaba yace da Muhseen

TSINTAR AYAWhere stories live. Discover now