*HANNA*.......💥
©Maryam Abdullahi(OumRamadan)
*47*
Hannu yakai ya bubbuga filon da take kai da karfi , bud'e ido tai tana sakin tsaki ta kalleshi a fusace tace "Malam lfy ina baccina zakazo ka wani tasheni, bashi kake bina kome?" Hade rai yay dan kar taga warginsa fuska ba walwala ya mika mata card din hannunsa , wani tsakin ta kuma saki ta fizge da karfi ta bude ta fara karantawa , "kan ubancan," ta furta tana hantsilowa daga kan gadon ta cakumosa da karfi tace "wllhy tallahi uban kuturuma yay kadan balle na makaho, ni zaka yaudara mk? Ni zakaci amana ?" Ta fad'a tana nuna kanta ,tai wani dariya tace "billahillazi sunan wannan auran lalatacce , kamar yadda na rusa wancan haka zan rusa wannan ,in zaka nemi aure sau dubu saina lalata sau dubu , saina zamar maka bakar Inuwa wllhy baka isa kamin kishiyaba da ajina d,,," bata karasaba ya wanke fuskarta da wani mari ta bude baki tana kallansa ya sake zabga mata wani marin, ihu ta fasa da karfi ya fizgota a fusace yace " zan buga miki last warning wllhy tllh naga kafarki a gidansu Jidda saina kusa sumar dake kinji na fada miki stupid kawai " ya hankadata yay wucewarsa daga dakin,
Wata irin dariya tai kaida ganin dariyar kasan ta takaici da bakin cikice ,card din ta dakko ta duba address din gidan , wata figalalliyar gown ta dakko tasa ta yafa vail a kanta ta d'au mukullin motarta ta fice daga gidan bayan tasa wani bakin glass da kana ganinsa kaga na rashin mutuncine,
Kallan gidansu Jidda take cike da kunar nai ta cije lips d'inta tai parking din motarta ta fito a fusace , da karfi take bubbuga get din gidan tana kunduma duk zagin da yazo bakinta , me gadin Yana budewa dama ta hankadashi ta shige ,
A compound din gidan ta tarar da Jidda ta rako wata kawarta suna magana , kallanta hanny tai ta zare glass din idonta ta nufi inda suke a fusace tace " wacece Jidda anan?" Jidda da tun da tazo wajen itama ta d'aure fuska cikin rainin wayo tace "ga Jidda nan , uwarme Jidda tai ake nemanta" hanny ta shaka a fusace ta kunduma mata zagi tace " ke karamar yar iska, yar tasha ballaga zuwanai nai miki kashedi akan mijina , wllhy in baki fita harkar mijina ba nice ajalinki , mijina yafi karfinki ta kona nafi karfin na had'a kishi da wata ya mace a duniyarnan , ba boka ba malam zan wulakanta rayuwarki idan kikai kuskuran sake kallan mijina,ya rage naki kiyi tunani in kuma kin shirya mutuwa yanzu to bisimillah" wata shewa Jidda ta saki kafin ta kalli hanny tace " shin uwarki data tashi auran ubanki bai sanar da ita mata 4 aka halastawa namijiba ? " bude baki hanny tai cikin tafasar zuciya ,Jidda ta cigaba da cewa "idan matsiyaciyar uwarki baka koya miki tarbiyya ba toni Jidda zan koya miki ita , gidanki kuma kamar na shigo na gamane idan har dabanci kike takama dashi to ni nan na takeki na cinye , nida aka haifa a bariki har kya nunawa karuwanci da burga ? To ki shiga hankalinki Jidda tafi karfinki wllhy ba Sa,ar yinki bace ni , zan bambamce miki aya da tsakuwa , gidanki kuma ki shirya inan tafe insha Allah da duk kalan zaman da kikeso ayi , shege ka fasa"
Hanny ta kai hannu zata cakumota da sauri Jidda ta kankadata ta kife a wajen sukai wucewarsu itada kawarta bayan sun tofa mata miyau,
Dakyar ta mike cikin tsananin tashin hankali ta shiga motarta sai sannan ta saki kuka , irin mugun kudurin data dauka akan Jidda ita kadai ta barwa zuciyarta , saita wulakantata kamar yadda ta wulakantata yau ,
Bangaren Hanna ko tuni ta warware , dan dama cikin bamai laulayinnan bane sosai sai kwadayi data Karo, kusan kullum mami sai tai mata abin kwadayi driver yakai mata , hakama aunty takan kirata taji ya jikin nata yake , uban gayyar ko ba,a maganarsa dan wani sabon tattali da kuluwa da yake bata , dan cikin nata sai yazo mata dasan sex sosai Wanda hakan ba karamin dadi yaywa haydar ba dan ko be nemtaba da kanta take nemansa , ,dama inya dawo gida ko k'ofar get bai sake lekawa indai ba masallaci zashiba , da daddare suna makale da juna tana jikinsa suke komai , saidai zatashi zai ajiyeta wai kar babynsa hanan ta wahala ,
Hanna ko tuni ta sake baje kolin shagwabarta son ranta , sai abinda takeso haydar yake , tattalinta yake sosai ,
Da yake week end ce yau tunda suka tashi ta saka masa rigimar ita gida takeso , tana kwance a jikinsa sai kuka take kana ganin kukan kasan zallan shagwabace , cikin lallashi yace "haba sweet kinsan banason fita week end ki bari ran Monday saina kaiki in na dawo daga office saina biyo na d'aukeki ko?" Turo baki tai ta mak'e kafad'a tace "aa nidai yau nakeson zuwa gsky" "pls banda yau sweet kinji" ya sake fad'a mata a hankali , tuni ta sake makalkaleshi dan yanayin yadda yay maganar taji tsigar jikinta na tashi ta sake sakin wani kukan , dariya yay a hankali yace "yanzu naji batu yarinya kice kawai jarabartakice ta motso shine zaki isheni da kukan gida" hararsa tai tace " eh din naji , aidai sadakina nake mora ko?" Lokaci d'aya ya fashe da dariya yace "eh fa lallai sadakinki , ki mori abunki dakyau yarinya " filo ta d'auka ta jefa masa ya cafe yana dariya , ta hade rai ta koma kansa ta ta dinga kai masa kanan duka a kirji dan kanta ta gaji ta bude baki zata fara sabon kuka ya hade bakinsu tsaf Yana kallan tsakiyar idanunta dake kara jefata a wani yanayi.
YOU ARE READING
Hannah
Historical FictionBincike a rayuwa wani abune da ALLAH ya hallata ku biyoni cikin wannan labarin na soyayya da kuma fadakarwa