32

977 55 11
                                    

                        *CUTARWA*

*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

32

Alhaji ya ce "Meye kuma na wata kwazgwamemiya baƙa? Ba mutum ba ce ba?"

"Ban gane ba mutum ba ce, ta girme shi fa ƙawar maryam ce?"

Ya ce "To shi ne me? Idan har shi zuciyarsa ta nutsu da ita ba shikenan ba, ni na yaba da tarbiyyar gidansu"

"Wallahi da sake, tun wuri ma dole a janye wannan maganar. Na zaɓa masa yarinya ya ƙi sai ya jajibo wannan mummunar yarinyar? Gidan da take zaune ai ba gidansu bane ba, zaman boranci ta yi a gidan kamar ƴar aiki"

"To kin ga kya samu lada ma, idan ya aureta ya kula da ita"

Kamar zata kama da wuta dan bala'i ta ce "Wallaahi ba zan lamunta ba, shi ne dan munafunci ni bai gaya mini ba, kawai sai yau ka zo mini da wannan zancen, a'a wallahi"

Alhaji ya ce "Ni dai in kin ga na fasa zancen auren nan, sai dai in shi ne ya dawo ya ce mini ya janye ya fasa, amma ba zan zama mutumin banza ba, shima sai dai in yi masa jagora ya je ya samu ubanta ya ce masa ya fasa"

Hajiya ta ce "Banda abun ki, ai ummi yarinyar kirki ce, nutsatsiyar yarinya ce, shi kyau ba shi ne abun dubawa ba, nagarta ake da cancanta ake dubawa"

"Kin ga malama ki rufa mini baki, ban saka da ke ba, idan nutsatsiya ce, ki haɗata da makakkun yaranki mana, sai ɗa na dama na san wannan duk kitumurmurarki ce, ke ki ka shirya wannan abun aka yi ban sani ba"

Hajiya ta ce "Allah ya baki haƙuri, nima ban san zancen ba sai yanzu, kuma su makakkun ƴaƴa ba laifi na yi wa Allah ya bani ba, jarrabawa ce, kuma da da nutsatstse a cikin su na yi sha'awar sanya ɗaya ya aureta"

Har mami za ta yi magana, Alhaji ya yi mata wani mugun kallo, hakan ya sanya ta yin shiru tana huci.

Hajiya kuwa tuni hawaye ya cika mata ido, tana jin zafin gori da cin mutunci da mami ke yi mata a kan yaranta, gani take yi kamar dabarar ta ce ta sanya Allah ya bata shiryayyun yara.

Alhaji ya kalli mami ya ce "Tun da kin saka mini mata kuka, sai ki bani wuri zan kula da ita"

Maganar ta sa ba ƙaramin fusata mami tayi ba, ta tashi ta ce "Haɗiyeta ƙarewar soyayya" tayi waje fuu rai a ɓace.

Ya dubi hajiya da hawayen fuskarta suka fara zubowa, ya rungumota jikinsa a hankali ya ce "You are brave woman, kar ki karaya, ki yi haƙuri ke ce fa mai Kwantar mini da hankali da rarrashina, ki yi haƙuri in sha Allah zaki ga tanadin da Allah ya yi miki sakamakon haƙuri"

CUTARWA!Where stories live. Discover now