33

887 65 12
                                    

                          *CUTARWA*




33
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

33

Tsit suka yi gaba ɗaya, suna jiran abun da Alhaji Tahir zai ce, dr. tamkar ya nutse saboda takaicin abun da kawu Ilyasu ya yi.

Alhaji Tahir ya yi murmushi ya ce "Ɗan uwa, ita bazawara ba mutum ba ce ba da ba za a kyautata mata ba? Shi ya ga yana son ta ai, ni mutum ne mai matuƙar ƙaunar ƴaƴana duk abun da suke so, sai ya saɓa wa addini ne zan ce a'a, amma dan bazawara ce ba shi yake nufin a aureta a wulaƙance ba"

Kawu Ilyasu ya ce "Ai dama kar ku ga an rufe ku ne, ku kallemu a matsayin mutanen banza, shiyasa na bayyana komai ko ba gaskiya ba? Kar ku zo a saka yaro yayi ta kashe kuɗi, tun da an ce shi bai taɓa aure ba, kar ya narka dukiya a auren bazawara ya zata budurwa ce, amma dubu ɗari biyar sun yi yawa a kuɗin auren bazawara, kar a cutar da shi"

Alhaji Tahir ya gyara zamansa ya kalli kawu Ilyasu ya ce "Ka san da wa ka ke magana kuwa? Bana alfahari da fariya, amma ko yafi haka ya bayar in kawo zan kawo, ba bazawara ba ko da tsohuwa ce kuwa, ka kuwa san wa ƴar ku zata aura ne? Da alama dr. Shikaɗai yayi binciken nan yakamata ya faɗaɗa muku bayanin waye Muhammad Raihan Tahir, zuriyarmu mun gaji yi wa iyali hidima. Ai ni da raihan ya ce mini mahaifiyar ta ƴar maiduguri ce, na yi zaton zaku yanka mana sadaki ne da sisin gwal, dan an ce auren ƴaƴanku sai jarumi" yayi maganar cikin barkwanci.

Dr. Da kunya kamar ya nutse ya ce "Ai kamar yadda na gaya maka, mu ƴan jigawa ne gagarawa, mahaifiyarta ce ƴar maiduguri"

"Allah sarki, to ace wa sirikata ina nan ina jiran turaren wuta, dan mutanen barno akwai ƙamshi"

Kawu Ilyasu ya ce "Kuma akwai ta'addanci da surkulle ba, ai da yake ma babartata ba wanda ya san a in da take yanzu, shekarun baya aka ce mana ta haukace ma"

Alhaji Tahir ya yi masa banza ya ce "Yanzu kun amince a kan watanni huɗun?"

Dr. Ya ce "Ubangiji Allah ya nuna mana, ya sa zamu gani"

Suka kammala, suka tashi suka tafi, suna tafiya dr. Ya dirar wa Iliyasu da bala'i.

"Wane irin mutum ne kai mara mutunci, ka ke tozarta yarinya a gaban sirikanta, wannan ai ba daidai bane ba"

"A'a yaya yahaya, haka shi ne kankaro mutuncinmu da kimar mu, haka kurum su gano daga baya, su ga mun zalunce su ai gara mu faɗa"

Kawu Saminu ya ce "To yanzu da ka faɗa ɗin me ya sauya?"

Cikin takaici kawu yahaya ya ce "Auren na ta na fari, ba a gabanku Idiris ya saketa ba, ko kusantarta bai taɓa yi ba ya ce saboda larurar da take fama, ya tozarta ta da bakinsa ya faɗa, da na taho da ummi daga gagarawa na kaita asibiti a kan larurar da take damunta, shi ma da bakinta ta tabattar babu mu'amalar aure a tsakanin ta da idiris ba ta da iddarsa.
Idan ka tona wa ummi asiri meye ribar ka? Sigar yadda ka faɗi maganar salon tozarci ne kawai, In da na gode wa Allah mutumin wayayye ne, kuma magana ake ta zunzurutun ilimi, kuma wannan maganar duk mun yi ta da shi, na gaya masa ummi bazawara ce ta taɓa yin aure, ya ce mini in dai ɗan sa yana son ta, shi ba shi da matsala da ita, kuma ɗaukakace kuna raye sai ummi ta yi ta, dan yaron manyan mutane ne, in sha Allah sai yarinyar nan ta huta.

CUTARWA!Where stories live. Discover now