44

593 36 3
                                    

                      *CUTARWA*

*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

44

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
44

Yayi ajiyar zuciya ya ce "Amma meyasa ki ka yanke wannan hukuncin?"

Cikin nutsuwa ta ce "Saboda na zama abun da ake so na zama"

"Me kenan?"

"Zaka ji daga baya" ta bashi amsa.

"Zan saya, amma dan Allah ummi kina ina, duk hankalina a tashe, Alhaji na daf da gano gaskiya ba ma tare, idan ya gano ina cikin matsala dan girman Allah kina ina?".

Ummi ta ce "Kai da zaka yi sabon aure, meye na damuwa da ni? Idan komai ya kammala ka tabatta ka taho mini da takardata, da zan nuna wa dr. Shaida, sannan ban ce ka gaya wa kowa mun yi waya ba, ka yi shiru da bakinka"

"Ummi.... Ta kaste wayar ta sakata a flight mode, dan kar ma ya sake kiranta.

Ta ƙurawa wayar ido, tabbas tana kewar raihan ɗin ta nesa ba kusa ba, ji tayi kamar ta yi kuka wannan abun da ta yi masa, gaba ɗaya zuciyarta babu daɗi amma dole ta ƙaurace masa dan samun cikakkiyar nutsuwa dan ta san da ya lallaɓata shikenan ba zata iya taɓuka komai ba.

Raihan yayi ƙoƙarin bin ummi, amma ta ƙi shiga wayar. Ya zubawa wayar ido yana lumshe ido, a hankali ya furta "Alhamdilillah, tun da kina lafiya"

Su kawu Ilyasu hankali ya ƙi kwanciya, saboda kuɗi babu su babu dalilinsu, gashi ba su san in da ummi take ba, balle a lallaɓata a rarrasheta su bata haƙuri, ba su taɓa zaton zata aikata abu makamancin wannan ba, yarinyar da suke wa kallon ko yatsa aka saka mata a baki, ba za ta iya cizawa ba.

Iya kuwa ta tsinewa ummi da mariya babu adadi, ta zageta har ta gaji, ba tare da ta ji alamar ta huce daga takaicin da ummin ta sanya su ba, ba ta taɓa tunanin ummi za ta aikata haka ba.

Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, wa'adin da kotu ta ɗibarwa su kawu ya cika, ba su da kuɗin da za su fitar da su ummi, dan haka aka saka gida a kasuwa, kuma Alƙali yayi musu faɗa sosai a kan illar jinkirta rabon gado komai ƙanƙantarsa.

Kamar yadda ummi ta buƙata, babu tunanin komai ko neman shawarar kowa ba, Raihan ya aika wani yaronsa gagarawa, ya ce zai sayi gidan, ba tare da wani ɓata lokaci ba, aka koma kotu, aka kai kuɗi Alƙali ya rarraba, aka bawa kowa nasa.

Sai dai duk ƙoƙarin da raihan yayi wurin samun ummi a waya, ya kasa ga gefe mami ta isheshi da ƙwarzaba a kan Safiyya. Ga ayyyka sun yi masa yawa, suna ta ƙoƙarin buɗe katafaren branch ɗin su na Abuja, hankalinsa ya rarrabu kashi-kashi.

Aka bawa su Iya notice na sati uku su tattara su bar gidan nan.

Saboda tsabar tashin hankali, ta yanke jiki ta faɗi aka tafi da ita Asibiti, aka yi ta sassaka mata ruwa.

Kowa ya fara tunanin bazama ya kama haya, sai dai aka rasa wanda zai ɗauki Iya, dan duk wanda aka ce ya ɗauketa, sai iyalinsa su ce su ba zasu iya da jaraba da masifarta ba.

CUTARWA!Where stories live. Discover now