49

712 51 5
                                    

CUTARWA!

AYSHERCOOL

(BRIGHT PENS)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION

https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

49

PAID ADVERT

*Hajiya ina zaki? Saurin me ki ke yi haka? Ɗan bani aron mintuna biyu kacal, na gaya miki albishir ɗin da na zo miki da shi. Shin ko kin san sirrin sheƙin fatar ummi, da ya sanya ta kama zuciyar MD raihan ta hana shi sukuni? Kai ba ma skin care ba, har da sirrin gyaran gashi, ina masu fama da amosani, karyewar gashi ko kuma sanƙo, jan gashi ne da ke? Ko taurin gashi kamar soson ƙarfe. Idan matsalar ki budurwar fata, tare da rashin glowing, Annur skin scrub da hair bliss sun shirya tsaf domin magance muku kukanku, me ku ke jira ku tuntuɓe su a kan lambar wayar su dan ƙarin bayani 07045971194 ko 08140450950*



49

Tsit kowa ya yi ya zuba wa mami ido, tana wani yatsune fuska.

Hajiya ta ce "Amma meyasa zaki ce haka? Wannan ai ba magana ba ce ba"

"Eh na faɗa, ko a dangina kin taɓa ganin irin wannan?, kalli kalar uwarsu ki kalli raihan ki kalli yaran".

Jajawur yaran, haskensu ya wuce ace hasken raihan kawai suka ɗaukko, gasu manya sosai, kuma kansu ƙwal babu gashi, kuma ba su da gashin gira ko kaɗan sai alamarta.

Mariya cikin jin kunya ta ce wa Hajiya "Bari na gansu"

Aka miƙa mata yaran, ta zuba musu ido tana murmushi sannan ta kalli mami ta ce "Hajiya, ai yaran nan da babansu su ke kama, haka na haifi ummi, Iya ta din ga ce mata aljana, sai dai kwana biyu kanta ya cika da gashi ko anty maryam, sai dai ummi tun tana jaririya baƙa ce".

Wani mugun kallo ta yi wa mariya ta ce "To ni danginmu babu irin wannan abubuwan, ni ban taɓa ganin jarirai a haka ba, danginmu dai kaf babu mai wannan farin"

Nan da nan Maryam ta harzuƙa ta ce "To mu namu akwai, duk tsiya dai ai na ɗanki ne ba wani ba"

"Ba ni da tabbas, ni ɗa na ma ba shi da cikakkiyar lafiya"

Hajiya da ta fara fusata ta ce "Ke dai ya rainawa hankali, dan ya tsallake son zuciyarki"

Mariya ce ta din ga basu haƙuri.

Raihan kuwa yana can ɗakin da aka kai ummi, sai zuba yake yi yana yi mata kalamai masu kwantar da hankali da ƙwarin gwiwa.

Likitan da yake yi mata allura ya ce "Maman twins ai ba Kya buƙatar maganinmu, wannan kalaman sun ishe ki warkewa" suka din ga dariya, sai da bacci ya ɗauke ta sannan ya tafi ɗakin da su Hajiya suke.

Noor ji take kamar ta kwaɗawa mamin raihan mari, ko karar ganin idon mariya bai saka ta yi alkunya ba.

Abdul da yake ɗakin ya tashi ya fita, Salim ma surutun ya ishe shi, ransa ya fara ɓaci.

Mariya ta kalli Salim ta ce "Salim, dan Allah jariran nan ba da babansu suke kama ba, dan Allah kar ki saka zargi a kansu tun suna jarirai, su sha wahala kamar ummi, idan ta tashi ta ji, ba za ta ji daɗi ba".

Salim ya ce "Mama, muna murna muna fatan Allah ya bawa ummi lafiya, mun gode wa Allah kyautar da ya bamu" ya ƙarasa maganar yana yi wa mami mugun kallo.

Kamar daga sama raihan ya shigo ya ce "Hajiya ba ni su na gansu"

Hajiya ta maze kamar babu abun da yake faruwa ta ce "Tun yanzu ka fara nuna wariya, ka tafi wurin matarka ko ɗaukar su ba ka yi ba" cikin washe baki ya ce "Tuba nake, dole in fara zuwa kanta, saboda su an yanka mini mata" yayi maganar ko a jikinsa yana ɗaukar su, wanda hakan ya sake ƙular da mami.

CUTARWA!Where stories live. Discover now