🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*HAWAN JININA*
~{UWAR MIJINA}~
🌀🌀🌀🌀🌀🌀
NA
*🤍Fahnaan🤍*_MARUBUCIYAR: MA'ESHERH(ANNOBA)_
©🎆
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* ✍🏻
_A• W• A•_
_{Al'umma writers, Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma, Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}._
بسم الله الرحمن الرحيم...*_Chapter 29_*
Na Fito da idanu tareda dafe kirji"Please Jaan Rufa mn asiri Wlh bazan iya ba,Ko a yanzu kunyar sa nakeji Bana iya kallon cikin idonsa ,Hakan kuma ba qaramin cikas ya jawo mn ba sai cutana yakeyi yana amfani da wannan daman wajen Cusa mn baqin ciki, please ki sake Tunani ni mafita nake nema ba wurin zama ba"
Jannan taja tsaki"Mtsww,Ke dama ba'a Abin Arziqi dake ,Tashi ki bani wuri " ta fada tana juya mn baya.
Jikina yayi Sanyi matuqa,Gashi NA farajin Qamshin Gaskiya cikin maganGanunta,Dafata nayi ta baya cikin muryan kuka nace "listen to me,Ba cewa nayi bazan iya ba,Kina ganin hakan shine mafita?,taya za'ayi ya Sakeni ta wannan fannin"
Janan ta juyo fuska dauke da kayataccen murmushi Wanda ita kadai ta San ma'anar Abinta tace " Neyfee, nima shaida ce akan yanda yaaAary ya tsane Ki, Ba cewa nayi ki bashi kanki ba,aah...Tada hankalin shi zakiyi Sai kinga ya fara Zaucewa sai ki Zame, ki yawaita shiga dakinsa idan hankalin Umma na Gareshi, kin Gane?, kar ki kwatanta hakan a Gaban Ramlah kinsan Sokuwace tanada Haquri yanzu Zuciyarta zata buga ta sheqa barzau, ki barta ta jida da baqincikin Umma" ta qarashe magana tareda kannemin ido daya.
"Lallai Janaan,Baki ta6a yin body contract da Namiji bane shiyasa kika ce nayi hakan, dama a da ne zan'iya Amma Gaskiya ni kunyar sa nakeji Sosai''
" Mtsww banza tsaya binta kunya bakisan Kudurinsa na hanaki Gayawa kowa ba, daga Kashe Ya Gama dake ya watsar,babu Wanda yasan da Aure A Tsakani ki shiga uku ki lallashe ,kina wana wani kunya sai kace ba Aure kukayi ba Ai cire kunyar nan zakiyi ki Ajiye ta Gefe Sannan Yi yanda nace kiyi daga baya kia Rufe kanki a daki kiyi taji kunyan ki ke kadai".
Nace"Haka ne fa, taya hakan zata kasance?, kinsan Hafsah bata Sani ba, kuma baaso tasani"
"Wannan ai mai sauqi ne,duk randa kin shirya Ki mn magana zan San yanda zanyi na dauke Hafsah ta kwana a Campus kinga sai kuci karenki babu babbaka"
Hararar ta nayi nace "Nifa har yanzu Gama yarda da wannan Shawarar ba, taya za'ayi na dauke hankalin sa da wannan kin sanshi da miskilancin Tsiya , wlh in yaaAary ne nan take zai 6a66allani babu Ruwanshi"
Janaan tayi dariya tana duba Agogon dake daure a tsintsiyan hannunta tace"naga Hafsah bata dawo ba Muje na baki Weapons na daukan hankalin namiji ko wayeshi ba miskili ba sai ya kwanto" ta fada tareda miqewa tana tattara littafin Gaban mu.
Muka Fito daga libraryn, A hanya take bani karin haske akan yanda zanyi yaaAary ya Sakeni cikin sauqi🥴.
"Munayferh Junayd"
Naji ankira ni ta baya,Waigawa nayi ina kallonsa, wani course mate din mu ne Wato badaruh an fi sannin sa da bhaddy,Yaron irin yarannan ne yan ithkan makaranta kuma Masu ji da kansu Irinsu ne bazaku ta6a ganinsa shi kadaiba saida Gang din sa Wato tawagar sa Masu taka masa baya.Ya tako har inda muke tsaye yana wani munafukin murmushi Cikin muryansa mai kamada na Yan daba yakalle janaan yace" Hy"
Tayi yar takaitaccen murmushi ba tareda ta amsa mshi ba,Bai damu ba ya juyo Gareni yace "Hawfar, Tun randa kika sa aka Kora mana banzan chan kika ware Kikayi wuyan gani Hope lafiya dai ko?, Duk ba ma wannan ba" ya kallemu up and down ya cigaba da cewa "Naga kaman Sauri kukeyi zan iya samun Koda numbern wayan ki ne?, Dan ina so na kiraki na karayi miki Godiya na musamman akan Gagarumin Aikin DA kikayi lallai kin chanchanci yabo,Dan haka duk mai son takura miki a Makarantar nan ki neme ni zan tsaya miki nida boys dna Koshi waye wannan tukuici ne a Gareki"

YOU ARE READING
HAWAN JININA (Uwarmijina)
AçãoLabarin Uwarmijin da ta Takura Wa surukarta, daga baya Ta hada danta Aure da Wata Yar Uwarshi saboda wata 6oyayyen kudurinta ,Amma me?, sai Yarinyar ta zamar mata Raina kama..........