23

9 0 0
                                    

Dec 20, 2020.

23

"Layla ta dawo ko?"

Naadir ya tambaya yana shigowa dakin, murmushi Mami tayi

"Bata dawo ba"

Ta amsa shi, kallon ta yakeyi da murmushi a tashi fuskar kafin ya wuce kitchen, bude-bude ya fara yana ganin wake da shinkafa, sai sauce din manja da ta sha kifi, yana zubawa yake fadin

"Layla ta dawo Allah Mami...ni na sani"

Dariya tayi wannan karin, da yake nan BUK Naadir din yakeyi, kuma duk a cikin yaranta shine makaranta take wahalar wa, saboda kokarin shi bai kai nasu ba, yana cikin gari amman ba kullum yake kwana a gida ba, musamman lokacin jarabawa irin haka, a makaranta yake kwana suna dan taba karatu, wani lokacin har tausayin shi take ji, akan Naadir ta yarda kokari halitta ne, amman babu wanda zaice baya fahimta, idan harka sakawa zuciyarka hakuri da juriyar bibiyar abu, hatta da Marwan tana kallon shi ya ajiye islamiyya, gashi da kokarin amman karatun bawai ya dame shi bane can-can. Yafi gane harkar kasuwan ci da yakan bi Yaya Ayuba.

Amman Naadir na zuwa islamiyya har yanzun, idan zaibi abu sau hamsin kafin ya fahimta baya gajiyawa. Yanda ake yaran suna gane Layla ta dawo har mamaki yake bawa Mami, shisa Naadir na fitowa daga kitchen din tace

"Wai ya ake kuna gane ta dawo ko baku ganta ba?"

Dariyar shi Naadir yayi

"Kamshi Mami, kamshin turare"

Dariyar tayi

"Wato ni bana saka turare kuke nufi ko menene?"

Kai Naadir ya girgiza, yana ficewa, Mamin su na kokari matuka wajen tsafta, amman turarukan da Layla take amfani da su daban ne, duk idan ka shigo zakaji su. Su suke fara sanar da kai tana cikin gidan. Sai kuma abinci da manja yawanci, su duka yaran suna so, ita kuma Mami bai dameta ba, kuma ba zata iya wahalar girki kala biyu kamar yanda Laylar takeyi ba, idan miya ce tana iya yiwa Mamin tata daban da babu manja, su kuma tayi musu mai manja. Kuma tana iya binsu a waya tana tambayar me suke marmarin ci, Mami abinda taga damar dafawa shi takeyi, ko Abbu baya mata zaben girki balle su.

Layla ma daga dakinta ta fito dan yunwa ta korota, tunda tayi azahar ta kwanta tana bacci, bata tashi ba sai da la'asar din, jikinta da yayi nauyi yasa ta watsa ruwa bayan ta idar da sallah

"Wai ina kike siyen turaren wutar da kike zuwa da shi? Yafi na nan da mukan siya dadewa a dakuna"

Mami ta tambaya

"Wajen wata Kamshi by Saffad, Anisa ce take zuwa da shi tana saka mana a daki, kamshin yana mun dadi, shine ta bani lambarta duk idan zan dawo nake siyo mana fa, kuma babu tsada Mami"

Layla ta karasa tana shigewa kitchen, sai da ta zuba abinci ta kai daki sannan ta daukowa Mami kwalbar turaren wutar tana dawowa ta kawo mata. 07010137848 Lambar wayar Mami ta duba, Layla kam yunwa takeji shisa ta koma cikin daki abinta, yau da ta tashi ji take a duniya idan bata ci miyar kifi da manja ba komai zai iya faruwa, shisa ta kira Jabir a waya tace ya siyo musu kifi. Da yake yafita kwadayi ko awa daya ba'a hada ba ya shigo dakin da kifi mai yawa, sai da ta saka wani a fridge ma. Abincin take ci tana duba text tsofin texts din su ita da Rayyan, ba sosai suke waya ba tunda ta dawo saboda Mami.

Shisa kusan wuni sukeyi suna musayar text, baya gajiya da saka mata kati ko da tace mishi tana da saura, yi yake kamar baijita ba, ta dai rasa ya zatayi da shi akan waya. Duk idan tayi mishi zancen waya sai yace ta kyale shi, ba zai barnar kudi ba akan waya. Kewar shi na danneta, in da ya siyi babbar waya zata saka shi ya dauko manhajar IMO dan su dinga video call ta nan, ta ga fuskar shi, ko hotunan shi basu kai goma ba wanda take da su, na ranar da ya gama jarabawa, sai kuma ranakun da yazo wajenta ta daga camera bai fisge wayar daga hannunta yana hada mata da rankwashi ba saboda zata dauke shi hoto.

HausanovelWhere stories live. Discover now