📕RAMIN KARYA
✍️Written by Khadija mustaphaWhatsApp 08022242200
Watpad khadijatmustapha25
Page 2️⃣2️⃣Kasa da kanta shukura tayi saurin yi cike da kunya dan bata taba zaton zasu hadu da salma touch ba , bakin rashin kunya ya mutu ne naji shiru sumaya ta fada tana dariya
Shukura ce ta hadiye wani yawu Mai daci sanan ta Kalli salma touch wace ta tsaya tana jefa ma shukura mugun kallo
Dan Allah Kiyi hakuri network ne wlh aman kinsan ni bazan gudu da kudin ki ba ko shukura ta fada tana hararar sumaya dake rike da kugunta tana kalon shukura
Salma touch ta yi shewa sanan tace ni Zaki fadama Haka Bayan kinyi blocking dina zaki wani ce ba gudu zakiyi da kudi na ba
Shukura shiru tayi dan tana barin Shagon a jiya ta danna mata blocking shiyasa koda salma tana kira bai shiga ba
Sumaya ce tace Allah Salma karki kyale yarinyar nan itace fa nake Baki labari yanzu tazo aron sarka ta da zuwan zataje kasuwa irinsa taje ta saka mun sarka a biki
Salma ae nima itace wace nake baki labari tazo shago tayi mun transfer din karya saida kudin kowa ya shigo Aman banga na wanan matar ba kuma nakira ashe tayi blocking dina sabida ita yar damfara ce
Sumaya ce tace ae wlh karki barta makaryaciya kawai ta fada tana kallon shukura
Salma ce ta Mike tsaye tana cewa ae tunda dai naganta ae dole a fito mun da kudina ta rike gyalen shukura tana mata kallon raini
Shukura ce tace baiwar Allah menene haka akan dubu 15 kike rike ni kamar wace ta miki sata
Karaf sumaya ta ce da abunda kikayi da sata mene bambancinsu shukura iyye yar rainin wayo kawai
Salma ce tace kinga sumaya wai ina ne gidansu ne naje nayi tijara tunda naga abun zaizo da raini
Ah gidansu ko gidan mijinta ae wanan da kike gani da ji matar aure ce ga gidanta can gida biyu ne ya raba mu
Salma ce ta saki shukura sanan ta tafa hanayenta ta rike habbar ta ta kalli sumaya cike da mamaki tace yanzu wanan da aurenta aman take wanan halin sanan ta juya kan shukura tace kekuwa baiwar Allah mene yakai ki aikata irin wanan abubuwan
Gasa mana da rashin godiyar Allah da hada kanta da mu mu manyan mata masu auren manyan mutane sumaya ta bawa salma amsa cikin gadara dan tabawa shukura haushi
Ae kuwa shukura ta shakka aman kamata da akayi ne ya Hana ta maida martani saidai zuciyarta dake suya
Salma ce tace kawata kina nufin masatyinta baikai bane ba
Fadi ki Kara kawata faci mijinta yake aman ita tace dangin dantata ne mudai bamu gani ba a jiki sumaya ta fada cike da izgili
Salma dariya tayi sanan tace kice ordinary matar Mai faci ce take fake life Kai wayoo ni salamatu
Kinga kawata kuje ta baki kudin ki ehe idan kin dawo na karasa warware miki zare da abawa
YOU ARE READING
Ramin karya (Hausa novel )completed
Short StoryYi sauri maza maza ki bani kayan nan kinga duk inda Aliyu yake yana kan hanyar sa ta dawo wa , kuma wlh yau ma ban tambaya ba na fito shukra ta fada Tana hada Kayan da ta zo Aro a wajen hafsa, uhm ae dole Nima nayi sauri Hafsa tace sanan ta cigaba "...