RUWAN DAFA KAI 2
Na SUMAYYA DANZABUWA20
cikin dare Abu ta farka saboda ciwon daya addabeta,tun tana iya jurewa har takasa,tasa kuka,don ko tashinshi ma kasayi tayi,sai kukan nata ne ya farkar dashi,ganinta cikin mawuyacin haline yasashi rikicewa batareda wani bata lokaci ba ya dauko Mata Abaya ya zura mata ya yafa mata dan mayafi,don yasan babu makawa abinne yazo,sai sannu yake mata bata ko iya ansawa,Amin ya shiga ya dauko bayan yakai kayayyakin nasu mota da ita kanta sannan sukayi asibiti.
Duk da dai cikin darane wajen karfe uku,amma ahakan ya kira Aunty Bilki,saboda koda yaushe saita jaddada mishi akan cewar daga sunga alamu fa su kirata,komin dare kuwa,to hakan kuwa akayi kafin kuce kwabo kuwa ta bayyana itada wata yarta,a asibitin.
Abu ana cen ana shan gwagwarmaya anata fafatawa,donma dai tana dan iya daurewa tayi adduoi,ga likitocin da sauran maaikatan wajen na bata baki,ana karfafa mata gwiwa,cikeda kulawa da tausayi,suma su yusuf din a wajen ba abinda suke shida su Auntyn banda adduoi,duk hankalinshi yabi ya tashi ya rikice,tanata dai kwantar mishi da hankali tana bashi baki akan komai zai kasance lafiya inshaallah,Allah yasa kawai yake cewa amma duk yabi yafita hayyaci, ya rikice da lokacin farida da yanzu bazamu iya banbance tashin hankalinshi ba.
Barmusu Amin din yayi ,aka bashi kaya yasaka shima ya shiga,bayan tun dazu dazaa shiga akace idan yanaso yashigo babu damuwa, yace aa,saboda tausayi bazai iya jure ganinta cikin wahala ba,toh yanzu dai hankalinshi ya kasa kwanciya yana ganin shigar tashi ce zata iya kawo sauki.
Yadda yaganta ne yasa zuciyarshi karaya duk ta galabaita kamar ba dazu suka gama hira ba tabbas haihuwar nan babu sauki dai,gashi bata masan waye akanta ba,amma dai fatanshi yanzu shine Allah ya raba lafiya,baisan sanda wasu zafafan hawaye suka fara zubo mishi ba,ganin yanata mata magana amma ko ansa bata iya bayarwa ita kadai tasan metakeji.
Har akayi Asubah ana abu daya dole yafita yaje yayi sallah yayi adduoin neman dacewa, sannan yadawo,amma shiru,hakan ne yasa yadinga cemusu suyi abinda yakamata sumata,tadaina wannan wahalar datakesha,idan akwai wani magani ko wani abu da zasu iyayi su mata,kallonshi suke kawai suma cikeda tsantsar tausayinshi dubada yadda yake masifar kaunarta,yakuma damu da ita,baabinda suke cemishi sai yayi hakuri ya kuma kwantar da hankalinshi haihuwar farice dole saitayi wannan dadewar takuma sha wahala tukun.
Kai abu,fa kamar wasa har ana neman azahar shiru,suma kuma lokacin likitocin sun fara tunanin mata cs saboda takusa wuce qayyadajen lokacin daya kamata,awa daya kawai suka kara mata akan indai har lokacin yacika bata haihun ba tofa saidai ayi cs din kawai aciro abinda ke cikin nata,don dan ma yafara gajiya bugun zuciyarshi yafara kasa.
Shi bama jinsu yake ba don bama gane abinda suke cewa yake ba,babbar damuwarshi itace kawai yaga tafita daga cikin azabar datake.
Agaskiya tashin hankalin dayake ciki yanzu yafi karfin tunanin mai tunanin,harda kuka don ba laifi shima akwai saurin karaya sai hakuri suke bashi ana kwantar mishi da hankali.Ai kuwa dai babu abinda ya chanja,mintina talatin cikin awa dayan daaka qayyade nayi,aka fara shirye shiryen shiga da ita,don idan aka ce zaa kara daukan wani lokaci komai yana iya faruwa.
Yanaji yana gani yasa hannu shaidar amincewa da yin aikin.Gani yayi alamun bakinta na motsi tanaso tace wani abu,cikin hanzari kuwa ya matsa kusa da ita,don jin mezatace,"mine mezaayi min?"tace dakyar hawaye wani nabin wani,hakan ne yasashi share nashi dasauri wai don karta gani,"bakomai,Cs zaamiki ki kwantar da hankalinki kinji"yace dakyar,"cs?to idan na mutu fa,ance fa ana mutuwa"tasake cewa,kukane yaci karfinshi yama kasa bata ansa amma bayason tagani hakan ne yasashi kasa da kanshi,"kiyi hakuri inshaallah bazaki mutu ba,zamu rayu tare har abada kinji,nima don ba yadda zanyi ne shiyasa zan bari ashiga dake bazan iya cigaba da jurar ganinki cikin wahala ba,gashi babyn yafara gajiya shima,"yace da ita cikin karfin hali,"Allah sarki,to kace suyi kokari su tseratar dashi,don Allah ni bakomai ma in na mut...."yayi saurin rufe mata baki,"ya zaki dinga magana irin wannan,kina wani zancen mutuwa kamar kin daina tausayina?idan kika tafi kika barni yazanyi"zuwa yanzu dukkaninsu kuka suke wiwi,gashi lokacin shiga yayi dama dan karasa shirye shirye ake shiyasa ma suka samu suna zantawa,"ina Amin"tace dakyar,"suna waje dasu Aunty""kace mata nagode"tace don zuwa yanzu ma an fara tura gadon nata,kasa jurewa yayi ya fashe da kuka,to yanzu idan tamutun fa dagaske ya zaiyi shi?komai fa na iya faruwa?babu abinda yadace yayi yanzu kamar addua, tubda dai hakanne kawai mafita a halin daake ciki.
Cikin sanyin jiki ya fito yanemi waje,yafara sabon kuka hakan ne yasasu Auntyn tsorata suma,"meya sameta?"suka fara tanbaya duk a tsorace,"bakomai"kawai yake cewa yana girgiza kai,bashi baki Auntyn tadingayi tana kwantar mishi da hankali amma ita kanta kukan takeyi,ganin kowa na kuka Shima Amin yafara nashi dama tun dazu yaketa tambaya ina take suke ta cemishi unguwa taje ita suke jira tadawo,su tafi gida,dakyar dai aka samu shi yusuf din yadan tsagaita da nashi kukan ganin babu mai rarrashin wani,sannan ya tashi yadan fita.
![](https://img.wattpad.com/cover/179970084-288-k235625.jpg)