Chapter 7

392 31 5
                                    


       🅿️145 to 150

" kundai shirya ko dan any time suna iya zuwa picking dinku so nizan tafi Aisha",
Yafada yana kallon Aisha yana yi yana satar kallon inda Asiya take tana ba afnan abinci,
Aisha na kwance tana lura da duk abunda yake faruwa sai dai bakin cikinta dayane meyasa Asiya bata taba sanar mata ba,
" Kodai tana sonshi kota fara yarda dashi jiyane ma kila taki" zuciyar ta ta jero mata wannan zantukan take taji gabanta yafadi,
Wani irin kishi da bakin cikine taji yana mamaye mata zuciya " Aisha nizan tafi",
Yafada tare da ajiye mata kudi agaba murmushi tayi ta kalla indasu Asiya take amma Sam bataga Asiya ba dan tunanin ta yayi nisa batasan tabar gunba,
Fita yayi yabarta da yara afnan nakuka da alama ruwa takeso wani haushine yakara rufe ta tuna kila yaje gun Asiya ne,
" Asiya! Asiya!!" Muryarshi taji yana kwada ma Asiya kira Jin yayi shiru yasa ta fahimci yaganta,
Asiya na kitchen yaji motsinta yashiga sai Jinta tayi ajikin mutum yana sussumbatarta Kota Ina kokarin kwatar kanta take,
" dan Allah Asiya ki bari zaki jima baki ganni ba please let me" yafada a cikin kunnenta,
Wani irin yarrr taji tundaga kafarta kanta duk jikinta jitayi sunmata nauyi inda takasa kokarin kwatar kanta,
Ganin haka yasa yakara rikicewa gun bin wuyanta da jikinta kukan da afnan ta kwala ne yasa Asiya takwace da gudu tafito kitchen din,
Amma saita kasa shiga dakin tsayawa tayi tana sauke su ajiyar zuciya tana dai daita kanta shima hakan ne yakasance bangarensa.

Fitowar sa kitchen din yasa Asiya ta ruga zuwa dakin inda ta tarar ya Aisha tadan rarrafo inda afnan din take,
Inda suka hada ido taga wani irin mugun kallon da yayar tata kema ta Wanda Sam bata taba mata shiba,
Sosai Tasha jinin jikinta " badai tasan meya faru ba" Asiya tafada a ranta,
" hmm yar rainin wayo nasan mekikaje yi keda shi sarae tabbas tsintacciyar mage bata mage amma zan...."
" to ni natafi saina dawo" yakatse mata tunani sanda ya daga labule amma idonshi tsab yana kan Asiya,
Ya Aisha ta lura dan har wani murmushi yake sosai abun ke Kara cin ta azuciya,
" na shiga uku" tafada a ranta Asiya kuwa kokarin dai daita sahunta take wani irin bugu kirjinta ke mata,
Sauke labulen yayi yadau Jakarsa yabarsu ranar Asiya sosai take ganin sauyi a idanun yar uwartata,
Ya ummi bata iso Kano ba sai bayan la'asar ta iso Asiya na girki tashigo da gudu Asiya taje mata oyoyo ta hankadeta,
" ke dallah sakeni banson sakarci" tafada tare da mika ma Asiya Jakarta karba tayi,
Tawuce bata jin dadin yadda ya ummin ke nuna mata banbanci Sam walh,
" hmmm sannu Aisha kawae wae kiyi ciwo amma wae dan wulakanci daga ke har shi kukasa kira kufada",
Shiru taji bayan tazauna yar uwar bata tanka mata ba,
" ke lafiya naga tunda nazo ko motsi bakiyi ba" tafada tare da taba Aisha amma still nan ma ba reaction,
" Asiya! Maza zo nan" Asiya dake girki Jin kiran yasa ta bar komai tayo dakin nan dai Asiya tamata bayanin ciwon sosai tayi kuka,
Amma abun haushi ta daura ciwon kan Asiya " hmm shiyasa nace karba turo miki wannan mugun irin gashi nan tazo yakawo miki ciwo shegiya",
Nan tayi ta aibata Asiya inda ya Aisha ma a ranta take kuma aibata tan tana ganin zuwanta ne sanadin komai gashi haarun dinta ya juya mata baya su sha kuka su duka,
Basu bar Kano ba sunbari akan sai washe gari.

" Faruk! Faruk!! Faruk!!!" Sunan da yaji Ana kira akansa kenan bai San inda Kansa yake ba Sam,
" Aayan please calm down and let us do our job" doctor din yafada tare da nuna ma nurse shi,
" kayi hakuri kadan bamu guri" tafada tare da dan janshi waje yana gani ta rufe kofa,
Aka kunna light din emergency " son what is wrong naji kiranka cikin kuka shiyasa nayi saurin biyoka" dad yafada,
Fadawa jikin dad yayi yana kuka " dad Faruk Faruk is not owk dan Allah kace su taimaki Faruk",
Mom dinsa dake gefe tausayin danta ne sosai yakamata dan sosai tasan irin abotan dake tsakaninsu tun yarinta sunzama kamar twins,
" please son calm down I promise you he will be fyn" sosai Aayan ke kuka kamar ransa zaifita,
" I will never forgive whoever hurt him walh i will surely catch that person" yafada da karfi tare da tashi jikin dad din yana share hawayensa,
" excuse me sir but inabukatarka a office" doctor din yafada sanda yafito dakin theater room din,
Sai a lokacin suka lura d the light was off angama kenan " doctor ya yake" Aayan yafada,
" dasauki but akwai abunda nakeson magana daku" tashi yayi daga jikin dad " muje" Aayan yafada,
" no son you wait for me here zakaji duk yadda mukai da doctor din" duk yadda Aayan yaso binsa sam dad yaki mom kanta tayi mamakin hakan,
Shiga office din yayi yazauna sanda doctor din yacire yar lab court din na shi da eye glass din ya ajiye gefe,
" doctor inafata lafiya" girgiza kai doctor yayi yana kallon dad,
" he is fine but muna bukatar sa hukuma cikin lamarin dan he is attacked,
" kuma a jikinsa was shot not long ago dan the wound is still fresh so inaganin yakamata musa hukuma ciki ayi bincike",
Tunda doctor yafara magana dad ba uhmm ba uhm uhm sai wani zufa dake karyo mashi duk AC din dake office din,
" Alhaji are you listening to me" doctor yafada yana kallon Alhaji, " uhmmm yes yes inajinka".

" bakace komai ba Alhaji" ciro handkerchief dinsa yayi yashare zufan tare da gyara zama,
" are you alright" doctor ya tambaya " yes kawae Ina mamakine" tura mai glass cup din dake gabanshi doctor din yayi,
" but doctor inaso kayi mun alfarma daya a yanzu ko nawa kake so zaka samu Insha Allahu",
Cike da mamaki doctor din ya kalleshi " bangane Alfarma ba mekake nufi" doctor yafada tare da kara matsawa yana kallon dady,
" inaso ka Adana maganar harbin tsakaninmu inada kwakwaran dalili kan hakan,
" sannan inaso kayi kokari karka saka police cikin wannan lamarin dan banson yarana su shiga cikin damuwa kan abunda basu jiba basu gani ba so ka Adana",
Mamakine karara akan fuskar doctor amma sai ya dake yace " to Allah yakyauta bakomai yadda kakeso din za'ayi amma ban bukatar komai",
Dady yayi da doctor ya fadi bukatarsa amma Sam doctor yaki yace bai bukatar komai agareshi.

" malam daga Ina wakake nema" kallon me tambayar nashi yayi da mamaki yana murmushi,
" nafeesat kardai kice baki ganeni ba" mamaki taji Jin muryarsa da yadda yaki sunanta,
" you got to be kidding me kambu farin wata sha kallo badai haarun dana sani bane",
Washe baki yakuma yana kallonta sama da kasa " wow gaskiya kinsauya duka kamar bake ba",
" malam inka fama hirar kabani guri layinane yanzu naga ba aiki kazo nema ba mtsw",
Cike da bacin rae nafeesat takalla gun da saurayin ke magana tayi tsaki "kaje anrufe interview yau sai wani lokaci",
Tashi saurayin yayi " hmm dama haka kuke inkunga Wanda kuka sani kubashi" nan dai aka kusa caccar baki,
Saida takira security suka fitar mata dashi agun,
Inda ita da haarun suka fice gun cin abinci dan hirar yaushe gamo.

KOREN MACIJITempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang