6

98 11 2
                                    

fitar su keda wuya suka haɗu da wani dogari suka tambaye shi ya musu kwatancen gurin

Gurin Sai ka fita daga sashen bayin ka ɗan yi tafiya kadan kafin ka kalla wani tafkeken guri, a cikin gurin akwai manya manyan dakuna (halls) sosai.
A kofar shiga suka haɗu da dogarai a tsatsaye suka tambaya tukun aka nuna musu hanyar da zasu shiga daya daga cikin halls din
Shigar su suka kalli kaya ne a jibge bila adadin
Karasawa suka yi suka bi layin har yazo kansu, sun tafka babbar Sa'a da aka basu kaya iri ɗaya wanda hakan ke nuna wuri ɗaya zasu yi aikin
Shudiyar zani ne da riga da dankwali kala huɗu huɗu da hijabai guda bibbiyu
Suna amsar kayan suka kama hanyar shiga sashen bayin kai tsaye dakin su suka wuce suka samu su Shafa'atu sun yi cirko cirko a tsaye kamar jiran shigowar su suke
'Jakadiyar Sarki yanzun nan ta zo bakwa nan zakuyi bayani ...'
Ai Lantana bata kaiga gama maganar taba aka bankado kofar Jakadiyar ce dai da dogarai guda biyu ai kafin su san me yake faruwa saukar dorina suka ji

Sai da suka jibge su iya san ransu har numfashi suke sauke wa tsabar mugunta kafin Jakadiyar Sarki ta ɗaga hannun ta alamar ya isa hakanan
'Na hukunta ku ne saboda kunje kunyi zaman ku,
Ko ahaka aka ce muku za kuyi bautar?, ai tunda Yarima ya kawo ku, kuda hutu sai naga dama'
Jakadiyar Sarki ce ke fadin haka
'Kuma wannan kaya me launin shudin da aka baku zakuna aiki ne a sashin Sarki
Da shike ku sabin zuwa ne ba sai kunyi sammako kun fita da sassafe ba amman ku fita da wuri'
'In kun ga dama ku wuce kuje madafar ku na bayi kuje ku karɓa abinci'
Ta karashe zancen nata tana yin ƙwafa kafin ta kade bujen ta tayi waje
'Sannu kunji?'
faɗar Shafa'atu kenan da tsigar tausayi
Nan suka taimaka musu suka mike suna jan jiki a haka suka je da ƙyar suka bi layin karban abincin nan ma kapın suka iyo hanyar ɗakin nasu

_________________

Yau ake saka ran dawowar Malam Sule me rini duba da sakon da ya aiko kwanaki cewar yau Litinin zai yi haramar dawowa
A gidan Malam Sule me rini an yi shara ba laifi kuma an yi masa girki.

Kamar yanda ko wanne magidanci yake tsammanin ya dawo ya samu gidansa cikin kwanciyar hankali da mutunci, to ba hakan ce ta kasance da Malam Sule me rini ba, sakamakon wani mummunan labari da yaji da saka kafar sa a cikin gidan nasa
"Toh yanzu Malam ya zai ji idan yaji halin da Hafsa take ciki kuma kunsan halin yan sarautar nan sarai ba......"
Ai Kulu bata ida zancen ta ba ta hango  Malam Sule me rini yayi mutuwar tsaye, Lawan ne ya taimaka masa ya ida jawo sa cikin gidan

" Me nake ji haka Kulu? Me kika ce?"
Malam Sule me rini ya tambaya
Nan Kulu ta ɓarke da kuka
Lawan ne yaja shi kan tabarmar kabar da aka shimfida masa ya taimaka masa ya zauna kapın ya dora da fada masa duk abinda ya afku
Malam Sule me rini yayi bakin ciki matuka na jin abinda ya faru
Abinci ma ba'a cikin hankalin sa ya ci ba kawai ya kashe yunwa ne. Nan take yayi ma gidan yayan sa, Baffa Musa tsinke.

Da shike Baffa Musa yasan komai nan suka sake tattauna wa akan za suje su Fadan gobe da sassafe talata kenan
Nan sukayi sallama Malam Sule me rini ya bada tsarabar da ya kawo wa yaran Baffa Musan

Komawarsa gida ya same su sunyi cirko cirko
"Me ya faru haka naga kunyi wani cirko cirko"?
Mallam Sule me rini ne yayi maganar nan
Lawan ne yayi magana
"Mama Zenabu ne ta suma"
"Kayi sauri ka kira Isah me magani yanxu"
Malam Sule me rini ne yayi maganar
Aiko nan take Lawan yayi maza ya fice daga gidan
Lawan be jima da fita ba ya dawo da Isah me magani
Bayan sun gaisa da Malam Sule me rini ya fara duba Mama Zenabu
An samu ta farfaɗo kuma jikin ta ya ɗan yi sauki

_____________

Da safe da misalin karfe tara Malam Sule me rini sukayi haramar zuwa fada tare da Baffa Musa da mai Unguwar su Malam Sule me rinin

Ba sune suka isa ba se wajajen goma
Da kyar da siɗin goshi suka samu suka haɗu da Sarkin fada
Suka sanar masa komai tare da fada masa in babu damuwa yayi musu iso gurin me martaba

Sai da Sarkin fadan yaga Lokacin shigewar me martaba cikin gida yayi bi ma'ana azahar, tukunna yayi musu ison shiga cikin fadan
Shigar su suka mika gaisuwa gurin Sarki
"Sarki ya amsa"
Suka ji wani bafade yace
Tukunna suka gaida manyan fada
"Me ke tafe da ku?"
Wannan bafaden da yayi magana da farko ne ya sake tambayar su
Sarkin fada yana gab da fara magana suka ji An kwada sallama ana neman izinin shigowa
Dogarin na shigowa ya zube a ƙasa yana kwasar gaisuwa

"Ƙiran gaggawa ya taso daga gurin Sarauniya babba (mahaifiyar Sarkin) tana neman Me martaba da Waziri yanzun nan"
Yana gama fada yayi ficewar sa
Ha ila yau wannan bafaden farkon nan ne yayi magana kamar haka
"Sarki ya bar ragamar aikin sa ma wa Galadima!?
A take fadawa suka tashi suka takewa Sarki da Waziri baya aka bar Galadima dasu Malam Sule mai rini
Nan kowa hankalin sa ya dawo kan Galadima
"Meke tafe daku?" Yayi tambayar yana kallon me anguwa
Nan take Me Unguwa ya sanar dashi
Budar bakin Galadima cewa yayi
"Wannan ba hurumi na bane kasancewar Yarima ne da kansa, amma zanyi magana da mai martaba nan da wata uku ka dawo dan a yanda ka bada labarin lallai yarinyar ka ita ce da laifi haka kawai Yarima da ba shiga harkan mutane yake ba bazai taso keyar ta zuwa horar da ita ba, kuma dalilin da yasa nace ka dawo nan da wata uku shine kapın nan ta horu, nikuma insha Allah kamar yanda muka yi magana dakai za'a fitar maka da ita"
"Godiya muke ranka ya dade" dukan su suka fada suna dukawa
Kawai Galadima daga musu hannu yayi

Tun sanda Galadima ya fara magana Malam Sule me rini yayi tagumi yana sauraron sa tare da share ƴar kwallar sa, daman yasan ayi haka yasan Hafsa batajin magana, amma Allah yasa hakan yayi sanadiyar shiryuwar ta

Nan suka sake godiya suka mike suka bar Galadima yana cigaba da solving ɗin matsalar mutane kamar yanda Sarki ya Umurce shi da yayi

___________________

Bayan sun karbo abincin su wato tuwo dan wannan dankararren taliyar baza a ce mishi abinci ba sai dai tuwon kam, suka zauna suna ci suna gabza uban kuka Shafa'atu ce take ta basu baki dan Lantana ko çıkan ku bata ce ba, ita a ganin ta ai iskanci ne ma, in ba hakan ba ta yaya kana bauta a gidan sarauta kace ba zaka jure duka ba? (Niko nace ai su sababbin zuwa ne)

Suna gamawa suka kama tattare dakin Sannan suka bi lafiyar gado domin mangariba da isha'i ma Shafa'atu ce ta tada su suka yi suna idarwa suke komawa suci gaba da bacci

Washe gari da safe bayan sunyi sallar asuba basu koma bacci ba gudun kar suyi wani laipin yasa suka bi layin wanka
A gurin layin wanka sai da Hafsa tajawo fada, dogarai kuma basu fasa dukan ta bah!
( Kujimin ja'irar yarinya gwara da Galadiman ma yace wata uku dan ko fara shiryuwar bata fara yi ba)

Haahhhhh
Bazan dena cewa ayi reading, commenting, voting da sharing bahh!
I lurvh you guys ❤️❤️

Nice nan
Fatima Idriss Bello
FADREES❤️

YARİMAN HAFSA Where stories live. Discover now