30

94 9 7
                                    

Ƙafar ta kasa daukan ta yayi, jin irin wannan baƙon yanayin kamar zata fadi yayi saurin riqe ƙugun ta da kyau, shima ɗin hakan ne, dan bai taba tsammanin zai iya yin hakan ba, be san me ya jashi ba, amma dai yasan abu daya, ya kasa controlling kanshi ne, sai da ya gaji dan kansa, kapin ya kyale ta, labban ta nada matukar taushi da laushi, kamar kar ya cika, kuka yaji ta saka ya juyo da fuskan sa saitin nata, ya mata kallon ki cigaba in gani?. Shiru tayi dan dole tana me kuntumo masa launukan ashariya a cikin zuciyarta, ya sata tayo alola suka yi salla, daga nan suka ci abinci, daman Hafsa yunwa take ji, tun tana fulako har ta saki jiki sai diban abinci take, nama kuwa anga na bati ai sai ta Allah kuma
Suna gama ci suka je suka wanke bakin su, suna shigowa dakin Hafsa tayi miqa zata kwanta a kasa, yace mata ta kwanta a kan gadon shi ba bacci zeyi ba, juya wa tayi ta kalli kan gadon, sai yanzu suka ga farin kyallen da aka shimfida musu akan ruwan tokan zanin gadon, dafe kai Yarima yayi cike da takaici, ita kuma Hafsa ganin ya bata dama, yasa take ta cire farin kyallen, toh ita daman ba sanin amfanin shi tayi ba, nan tayi kwanciyar ta, ta juya ma Yarima baya, idan kuma ta tuno da abinda ya faru ba da jimawan nan ba, sai taji kamar ta nitse dan kunya, ikon Allah, wai yau ita da Yarima🤭 sai kuma tayi shiru, kan ta ankara bacci yayi awon gaba da ita sai aikin birgima da take saki.

Shi kuma Yarima tunani yake tayi, yana so ya kamo bakin zaren da ya sa wadanda ze aura suke mutuwa, zama yayi akan gadon yayi tagumi, can dai ya yanke shawarar zeyi maganan da Sulaiman, juyawarsa keda wuya yaga Hafsa tayi miqa zanin ta ya taho cinya, fara ƙare ma fararen cinyoyin ta kallo yayi, daga bisani ya saka hannu ya ja mata zanin ya rupe mata, kashe fitilan dakin yayi kapın ya kwanta ata daya gefen, shima da tunanin abinda ya auku dazu bacci ya dauke shi dan gaskiya yau yaji kunya, baiwar sa ta samu daman raina shi, domin ta kalli gurin baccin sa.
Yau ne a rayuwarsa ya taba kwanciya da mace a gefen sa, sede wannan ba kwanciyan dadi bane domin Hafsa kafa ta dinga ɗora masa daga karshe ma, akan sa tayi masauki, yana jin ta ya kyale ta, daga nan kuma bacci mai nauyi ya dauke sa, har saida ya makara sallan asuba,
______________

Injiniya ne a kwance a dakin sa, yana ta faman zubar da hawaye, yana matukar san Hafsa, so ma na hakika, amma gashi yanzu ƙaddara ta raba su, ko da mahaifiyar sa ta masa maganar Abinda yake damun sa, sai bai boye mata ba, ya fada mata hakikanin gaskiyar abun, nan ta dinga lallashin sa, daga karshe dai izini ya nemo a gurin mahaifinsa kan zai koma ƙasar Mali yaje ya sake bunƙasa karatunsa na injiniyanci, ko da mahaifinsa ya amince, da sassafe yayi sammako yabar Bauchi, kunji inda ta injiniya ta kare masa.
______________
Kilishi ce durqushe a gaban Boka Kapoor, dariya mai kama da kukan zaki ya saka, yace mata "abinda yake ranki muma bamu gani a allon sihirin mu ba, da baza mu bari ayi auren nan ba face saida gawan ta, gashi sharadin abin namu, kapın aure za'a ke kashe matan, yanzu kuwa da aka samu akayi auren, zamu samo mafita, domin muma faduwar mu ne ba ke kadai ba, saboda jinin sarakai dadi garesa, yanzu muna hada wata magani da zai dauki watanni kapın a gama hada shi saboda hadarin sa, sai an samu ruwan maliya kapın haduwar maganin ta kammala, domin sai aljani mai shekara dari ne kadai zai iya debo ruwan sbd haka da an gama za'a baki ki sa mata a ruwa, daga nan zata yi sallama da rayuwar ta, shi kuma za'a maida shi mara karfin iko, domin za'a kwace masa matsayin sa na Yarima Mai jiran gado. Ɗan waziri kuma za'a saka masa cuta da zata yi sanadiyar shi, amma sai na ita yarinyar ya kammala kapın.
Da jin haka tasan boka ya gama maganan sa, sbd haka ta dawo tana saƙa da warwara.
Zata aika baiwar ta, tana sa mata ido akan matar da Yarima ya aura. (Har yanzu su Kilishi basu san cewar wacce Yarima ya aura baiwar can bace, wato Hafsa.)
______________
Sulaiman kuwa ko da yaje ya samu amaryar sa ta jima dayin bacci ga nan farin kyallen da aka shimfida musu ko yaye shi bata yi ba akai ta kwanta abinta, sai shi kuma bai tada ta ba, shi Wallahi mamaki ma yake, idan aka ce masa zai yi aure nan kusa wlh musawa zai yi, sannan ma a rasa wa za'a hada shi auren sai Bilkisu kanwar bayansa, ai wlh shikam tashi ta gama karewa dan raini kam ta gama raina shi. Allah Sarki, gata yarinya kyakkyawa kuma tana da hankali despite cewar ita yar sarki ce bata wulakanta bayi, In Sha Allah alkawari ya dauka kan zai kula da ita. Miqewa yayi yaje gefen ta ya kwanta, tare da dora kanta a saman kirjin sa, sa'annan ya kashe musu fitilan dakin.
______________

Yarima ne bai farka ba saida yaga haske ya fara fitowa, da farko da ya tashi yaji an riqe shi sosai, har ba ya iya motsawa yayi yayi ya kwaci kanshi ya kasa, dan wuyan shi aka rungumo sosai da sosai, wanda har hakan ya fara basa wahalan numfashi, mamaki ne ya kama shi dan shi shaff ya manta wai an masa aure jiya, sai da ya ware idanun sa da kyau ne ya ga ashe Hafsa ne ta shaqe se, dakyar dai ya samu ya kwaci kansa yayo alola sannan ya tada ta, saida tayi ta sumbatu sannan ya samu ta tashi, wannan dai da wahala kawai aka hada shi, tana shiga makewayi ya tada kabbara, can se gata ta fito ta fara sallan ta, da ta gama ta gaida shi se da yayi kusan minti Uku kapın ya amsa, ganin yana ji da sarautar sa ne, Hafsa ta tashi ta haɗa masa ruwan wanka, da yayi ita ya sata ta shirya shi, sai kanne kanta zuwa kasa take tayi, gama shirin shi kenan itama ta shige taje tayi wankan, Seda ta gama ya nema abinda zata daure jikin ta ta rasa, gashi Allah ya gani baza ta iya maimaita kayan da ta cire ba, dan lekowa kadan tayi, sai kuwa suka hada ido, gira daya ya daga mata alamar tambaya, sai tace masa dan Allah ya miqo mata kayanta, shi kuma a ransa cewa yayi lalle yarinyar nan taga gurin baccin sa, wato shine ma zai miqa mata abinda take so, ranshi a dan bace ya miqo mata hijabin sannan yace mata kayanta suna dayan dakin, yana fada mata haka ya miqe yayi gurin kofa, har zai fita ya canza shawara, ya tsaya daga jikin kofan ya harde hannayensa, ganin haka da yayi ranta sai ya ɓaci, tun farko yasan akwai wani daki shine bazai fada mata ba?
Fitowa tayi tana jinta a tsarge dan hijabin da ta sa ji take kamar yana bayyana suran jikin ta, tana fitowa sai tayi hanyan kofan dan taje dayan dakin ta sanya kayanta, tazo wucewa ya tare, sai tabi ta gefen sa ta tafi dayan dakin, duk tana jinta sukuku, tana shiga tayi hanyar durowan kayayyakin cikin dakin, ilai kuwa, nan taci karo da kaya masu yawan da har saida ya bata mamaki, in za'a hada kayan ta na gida dana Dije da Azima da Jamila duk baza su kai wannan yawa ba, ciro wani doguwar riga tayi dan ta sa, Yariman da bata san da shigowar sa ba ya riqe.
"Ni zan sa Miki tunda Nima ke kika sa min" ta tsinci muryar sa, karkarwa ta fara yi kapın tace "Ni bana so ai kai kace in sa maka, sannan ba'a san raina na sa makam ba, saboda haka Ni bana so" ta karashe tana mugun hade rai dan haushin shi take ji, shidai bai sake ce mata komai ba sai kokarin yaye hijabin jikin ta yake, ihu zata sa masa ya rufe bakin ta da nasa, nan ya fara aika mata da wasu irin zafafan abubuwan da bata taba sani ba, hannunsa taji yana yawo a jikin ta, sai kokarin kwace wa take amma ta kasa, sallaman da suka ji an doka ne, ya tsayar da Yarima daga abinda yake shirin aikatawa, fita yayi yana me saita kanshi, sai yaga ashe jakadiya ce, duqawa tayi ta basa gaisuwa kapın ta fada abinda yake bakin ta, wanda lokacin yayi daidai da fitowar Hafsa
"Allah ya ja da ran Yarima, Kilishi ce ta aiko Ni akan in tafi da farin kyallen za'a je a nunawa sarauniya babba".

Gaskiya bana ganin votes
Sannan kar ku manta kuyi following account din nawa.

YARİMAN HAFSA Where stories live. Discover now