12

72 5 0
                                    

Gobe ya kama Asabar ranan da za'a yi gasar da ake ta tsumayin zuwan ta, tun ranar laraba sarakuna suka fara zuwa,
Jiya juma'a kuwa ko wane sarki da ake expecting zeyi participating shida mutanen sa sunzo. Manya manyan ɓangarori aka ware ma sarakunan suka sauka da tawagar su.

Hafsa na hango tana bin Yarima kamar jela, duk inda ya saka ƙafarsa itama nan take saka nata, ko wane aiki ita yake saka wa, ba ƙaramin azaba Yarima yake baiwa Hafsa ba, amma in ta tashi abun ta, yi masa take yi bata jin ko ɗar, to tasan karshen ta yace ze sa a zane ta ne, ko a hana ta abinci. to amma dukan har an gaji an kyale ta, yanzu idan tayi abu a cikin sati biyun nan da suka gabatar tare sede ya sa mata ido, gashi shi ba mutum bane me san magana.
Ranan da ta kular dashi shaqe ta yayi har seda yayi danasani dan har suma tayi amma da ta samu kanta, abun nata gaba ma yayi.
Ranan da taqi zuwa aikin nan da taje kusan kashe ta wani dogarin sa yayi da duka amma ina Hafsa ce pa. Sede kuma tana aikatuwa iyakar aikatuwa.
Hutu da take dashi se in bacci ne ya dauke shi amma ko tsinke ze dauka ko da kuwa yana kan cinyar shi ne, se ya kira Hafsa ta miqa masa. İyakacin ta guna guni ne, idan ta harzuqa sa kuma ya sa a zane ta.
Tasha kwana a sashen shi saboda yawan aiki dayake saka ta, wani abun ma is unnecessary amma se ya sata tayi shi. Murja kam har tausayin Hafsah take yi amma ita kuma sam kamar abun be dame ta ba.

Yanzu ma fitowar su kenan daga sashen mahaifinsa suka yi kiciɓus da wani ɗan Sarkin Gobir da ya nace wa Hafsa, idan ya hango ta yayi ta kallon ta kenan, ranan da ya ganta ita daya ya tsayar da ita yana ta jan ta da labari tana murmushi sega Yarima kamar an jeho shi, shida Suleiman, hakikanin gaskiya ransa yayi matukar ɓaci daya ga Hafsa tana murmushi, shipa ya tsani yaga tana cikin jin dadi, daga kai yayi yaga ɗan Sarkin Gobir din yana mata wani irin kallo, se yaji ransa ya ɓaci, ta ya za'a yi baiwar sa me yi masa aiki zata tsaya tana kula wani sakarai? Gaskiya hakan kamar zubewar aji ne a gareshi.
Ranshi a mugun bace yake kallon su su dukan su, shi kuma ɗan Sarkin wanda yake da suna Isma'il, se zuba surutu yake can da ya daga kai yaga Yarima da Sulaiman din, a take ya mika musu hannu suyi musabaha, Yarima yaqi bashi hannu, shiko Sulaiman ya basa nasa, a Lokacin Hafsa ta dago idon ta suka hada ido da Yarima, jikin ta har kyarma yake tsabar rudanin ganin irin kallon da Yarima yake aika mata.
Budan bakin Isma'il keda wuya yace "Gaskiya Yarima in zan koma masarautar mu dole ku bani Hafsa domin ta kwanta min a rai".
Se a lokacin Yarima yasan sunan ta Hafsa, wani kallo ya mata ai bata san sanda tabar wurin ba ta koma sashen su.
Shi kuma Yarima se ya share shi, shidai Sulaiman abun mamaki ya bashi, babu yammata ne a Gobir da zai ce wai abashi Hafsa?
Musabaha suka sake yi da Sulaiman sannan suka wuce sashen Yariman daman can zasu je.
Yarima ranshi in yayi dubu to ya ɓaci. Gaskiya Isma'il ya rena sa, har yaga baiwar sa yace ta wani kwanta masa a rai? Jikin sa har rawa ya soma yi se daga baya ya dawo da hankalin sa, nan da nan yayi murmushi tuna irin matakin da ze dauka.

Yanzu kuwa da ya ganshi se ya kara hada ransa, ido ya mata akan ya sallame ta ita kuwa ta kama hanyar zuwa sashen su na bayi, a hanyar ta na komawa ta sake haduwa da wani.
Farko ma ce mata yayi wai tana matukar kama da wata wanda ya sani. Dariya tayi masa tace se dai kama, amma bawan Allah ya sha gaban ta wai shi be yadda aiki take a masarautar ba
"Haba dai kyakkyawar budurwa kamar ki ace tana aiki a matsayin baiwa? Gaskiya da sake" inji matashin me suna Ibrahim da fada.
Ita dai Hafsa share sa tayi, tayi tafiyar ta taje ta samu Murja tace yau an sallame ta da wuri.
Murja dai ta tsaya tana mamaki, tace "Gaskiya Hafsa ban yadda ba, kodai ya baki yancin ki ne, ya sallame ki baki sani ba, in ba haka ba, yaushe rabon da ki zo iwar haka"? Murja ta karashe zancen ta cikin tsananin mamaki domin gaskiya Yarima yana matukar horar da Hafsa, ko gasan nan da za'a yi, ita ya barma ragamar komai, sannan tsabar tsugudidi wai har se yayi bacci tukunna ya yarje mata taje tayi bacci.

Ita dai Hafsa kwanciyar ta tayi ta shaqi bacci, se chan da Murja ta dawo daga sashen me martaba take ce mata wai Yarima ya aiko yana neman ta, lokacin marece ne lis, tashi tayi tana zumbura baki ta dauki kallabin ta tayi waje, ita fa in ba Sallah zata yi ba bata daukan hijabin da aka basu, ji take yana takura ta, sannan ma yau yana daga cikin ranakun da bata Sallah.

Sashen Yarima ta nupa, babu sallama ta kutsa kai, nan taga dakin shakatawan nashi a cike da matasa, da abinci iri iri a zube a tsakiyar dakin, ga abubuwan sha, ga kayan marmari iri iri, kayan jikin matasan kadai ya isa ya nuna maka ko su wanene, daga ido tayi ta ganshi a kishingide akan tumtum ga su Suleiman da su Hayatu ata gefen
"Salamu Alaikum" ta tsinci kanta da yin sallama, se gaba daya hankalin su ya dawo kanta, se ta ɗan ji ta a takure saboda rashin saka hijabin da bata yi ba, nan take ta zube har kasa ta kwashi gaisuwa a gunsu, ƙalilan ne suka amsa se ismail da ya zuba mata na mujiya can se kuma ta yanke shawarar taje gurin sa, isar ta gun nasa seda ta ɗan duqa ta gaida shi ya amsa a yamutse.

Ganin har yanzu idon samarin nan na kanta ya sa Yarima yaji ransa ba dadi, se yaji kamar ya sa ta ta koma amma se ya basar
Alama ya mata da ta shiga uwar dakan shi ta gyara
Shigewa tayi kan Isma'il kamar ya lanqwashe tsabar kallo idon Yarima kuwa kyam akan shi. Nan ta tadda dakin a hargitse ga kaya dinkim akan gadon, ta ma rasa ta ina za ta fara, ga takalma nan birjik suma a zube, nan ta fara mita
"Gaskiya wannan Yariman akwai shi da kazanta, dubi dan Allah yadda yayi da dakin nan se kace wani karamin yaro fisabilillah gashi ba daman ka masa magana yanzu ya sa mugayen azzalumin fadawan san nan su duki mutum a banza, daman na lura sam zuciyar shi babu hasken imani, mummunan Yarima kawai....."

Juyowan da zata yi bata karasa ba ta hange shi yayi folding din hannun sa biyu yana kallon ta, ita sam bata san sanda ya shigo ba ai da tayi shiru, ƙafan ta ne ya ɗan fara kyarma amma se ta kafse, tana hura hanci.

"Maimaita abinda kika ce" ta tsinkayi muryar shi a setin fuskan ta, karasowa yayi daf da ita kamar wanda ze hade fuskan sa da nata, a matukar tsorace ta fara jan baya, kapın ta ankara taji ya janyo hannun ta ta fada jikinshi se karan abu suka ji Dummmm.

Let's meet in the next chapter

Read
Vote
Comment and
Share.

Fadrees🖋️🖋️.

YARİMAN HAFSA Where stories live. Discover now