MARAICHI

1K 59 0
                                    

🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                             🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
            NA
  Zainab Naseer Sarki
    (Zeenaseer😘)

1⃣0⃣

Haka ta mike taci gaba da abunda take ranta duk ba ddi.

Shima yana fita gidansu ya nufa dan yasamu yayi breakfast dan ba sosai yakesan cin abinci restaurant yafisan na gida.
Dan yanzu kam Har mummyn shi ta gaji da magana akan matarsa.
Shima kuma bashi da burin kara auran,tunda yanzu ga guda dayar nan ta takura masa bashi da sakat akanta.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Tana kwance kan gadon su dan yau gaba daya tunda ta tashi batajin ddi cikinta keta faman ciwo.
Babu abunda tayi dan tana jin ko makaranta bazata iya zuwa ba.
    Hafsat da ta lura da hakan ta karaso kusa da ita tareda fadin Sapna lafiyarki qlau kuwa.
   Wallahi ya hafsa tun jiya da magriba nakejin jikina babu ddi ga ciki na sai faman jiwo yake.
   Amma kuma bakiyi maganaba aida na baki magani.
   Itade shiru tayi dan batajin ddin yin maganar ma.
    Toh ko kin fara period ne.
   Dayake tasani tunda ana koya musu a makaranta.
    Girgiza mata kai tayi tareda fadin aa.
   Nazata kema kin fara dan naga Safiya nayi.
   Yanzu kije kiyi wanka ki shirya tunda makaranta zaku tafi.
    Zandeyi wanka Amma ya Wallahi banjin zan iya zuwa makaranta.
   Toh tashi kije kiyi inyaso saiki karya kisha maganin ko kuwa.
    Mikewa tayi ta nufi toilet din tareda fadin toh.
    Tana shiga ta hada ruwan wankan.
   Tana cire kayan jikinta taji kamar pant dinta ya jiki.
Ga mamakinta tana dubawa taga jini ta dan tsorata duk da tasan komai game dashi amma gani take kamar yayi yawa.
    Leda ta dauka ta saka aciki sannan ta sa cikin dustbin.
   Saida tayi wankanta tsaf ta gama sannan ta fito daga toilet din gashi batasan yanda zata fadi maganar ba dan tana sana gayama ya hafsa ta bata patt.
   Yauwa kin gama hafsa tashigo dakin tana fada yauwa ga maganin nan da abinci inkin gama saiki sha kingani makaranta zan tafi safiya ta tafi.
    Toh! Ya hafsa dan Allah amm dan Allah nima ki bani dama yanzu da zanyi wanka na ga jinin yazo.
    Murmushi tayi tareda fadin kice in matan mama an girma tana dariya ta nufi wardrobe ta dauko mata always sabowa ko budeta ba'a yiba.
Sannan ta ce mata gashinan kinsan yanda ake sawa kona koya miki.
    Kanta akasa dan kunya takeji take na iya.
   Yawwa yr kirki gashinan to kisaka da kinji ta jike ta fara damun ki,saiki canza kisaka wata ita kuma ki saka cikin leda ki kai dustbin din waje karki anje cikin toilet.
    Toh nagode yaya saikin dawo.
    Tam! Natafi tafada tare da fita daga dakin.
    Murmushi tayi tareda janyowa ta duba ta sosai sannan ta sanya ta saka kayanta ta gyara gashinta dan tayi tsifa ba'a mata kitso ba.
    Tana cikin karyawa taji Umma na kwala mata kira dan taga bata je makaranta ba.
   Da sauri ta anje abincin ko magani bata shaba ta mike ta nufi dakin nata.
    Tana shiga Abba tagani zaune kan kujera gabanta ne yayi mugun faduwa dan duk duniya babu wanda ta tsana kamar sa.
    Zaune yake kan kujera yana dan wayar shi yaci magani ko murmushi baya yi suna hira da Umman tashi jefi jefi.
    Asanyaye ta shigo dakin tareda durkusa ya ina kwana!
    Ko kallan idan take beyiba bare ya amsa mata sallamar ta.
    Sannan ta jiyo ta gaida Umman.
    Lafy kawai tace da ita bata kuma mata magana ba Har ta fara gajiya da tsugunnan da take sai can yace.
     Kinsan bakije makaranta me ya habaki zuwa kiyima Bilkisu abunda zakiyi mata.
     A zuciyar tace lallai ku din nan inba doleba me zai hanani zuwa makarantar dama na sani nayi tafi yata maybe danafi samun kulawa.
    Ba magana ake ba magana ake mikiba kina jin mutane kinyi shiru.
    Firjita tayi tareda fadin Umma Wallahi bani da lafiyane shiy...
   Tsawa ya daka mata wata ta sanyata mikewa zata gudu.
  Dawo nan ki tsaya ya nuna mata gurin da zata tsaya kusa da shi.
   Gaba daya jikinta rawa yake gaba daya ta nemi Ciwan ta rasa.
  Ubanme yake damun ki?
    Batasan Lokacin da tace babu komai.
   Wato mu sa'anin was an kine ko?
   Hawaye ta fara ta hada hannayanta tareda fadin dan Allah yaya kayi hakuri Wallahi ba karya nakeba.
   Naji huce waje kiyi frog jump kuma banasan ki dena saina fito.
    Da sauri ta durkusa tareda rike kafafuwansa tana kuka dan Allah yaya kayi hakuri Wallahi cikina ke ciwo kuma idan nayi muguwa zanyi.
   Banza yayi da ita tanata faman kuka agabanshi.
   Ita kuwa Umman tashi tayi ta shige dakinta ko ajikinta.
    Tashito kibar gurin nan kuma kafin na shigo kin gama mata komai.
    Jikinta Har barri yake tace toh.da sauri ta mike kai tsaya part dinsa ta nufa Dan kota maganinta batayi ta nufi dakin.
    Koda ta shiga falon kamar anyi party yayi kace kace gaba daya ko ina an lala tashi.
    Batasan ta inda zata fara aikinba.
    Tana nan tsaye Rahama ta fito daga ita sai pant da bra ajikinta.
Ta zuna kan kujera tana kallan Sapna.
    Da sauri ta rufe idanunta da hannunta kirjinta na bugawa.
    Cikin wata muryar tace meya haka Sapna zoki zauna inasan magana dake.
    Kasa ko motsi tayi daga inda take.
    Shikenan tunda bazaki zoba ni bara naxo...

😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷

Written by Zeenaseer😘

MARAICHIحيث تعيش القصص. اكتشف الآن