💖💝BATUUL 85💖💝

8.9K 488 20
                                    






Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR*



      Cikeda masifarta take kallonshi, shiko karasowa yayi hannunshi cikin aljihun wandonshi yace "Sit!, magana zamuyi", kallonshi ta tsaya yi a tsagere kamin ta zauna ganin duk ya canja mata kamar ba Idrees d'in dake shakkarta da gudun b'acin ranta ba, wanda in ta fad'i abu jiki na rawa zai d'auki maganan, had'e rai tayi ta dake tace "Wai kai yanzu sabida tsabar wulakanci kan wadannan tsinannun kayan naka kasa na taso na baro muhimman  abubuwan da  nakeyi a Abuja na taho Lagos?, toh wlhy yanzu maza maza ka kwashe tsiyarka kuma gyaran ma ni ba irin wannan nace maka  inaso ba ai", ba yabo ba fallasa ya fara magan yace "Tun baki san kayan mene ba kike wannan b'ab'atun, toh kaya dai nakine in baki sonsu ki zubar dan haka al'ada yace min kuma itama d'in haka nayi mata", katseshi tayi da hannu tace "Kayi wa uwar wa irin wadannan kayan, dan cin mutunci irin naka ma ba ni kadai kayiwa wadannan kayan ba harda had'ani da banzaye, nasan bazai wuce wad'annan masu kafar sauron bane da ke yawo a cikin gari kayi mana tare dasu, nasha fada maka ka dena had'ani da wadannan matsiyatan kana mana kaya tare......", bata rufe baki ba sai ji tayi yace "Aure zanyi next week, Kayan fad'ar kishiya ne gashinan snn wannan yawon naki daka yau kin barshi kenan, in har badaa izinina kika fita ba toh koma inane kikajeshi karki dawo min gida, kiyi zamanki a can", brain d'inta ne ya dena functioning for a minute, kamar a planet Neptune take jinta sbd yadda taji tana yawo saman iska, komai na juya mata, ido kawai ta zuba tana kallonshi har saida hankalinta ya dawo snn ta miqe tana cire duk wani abu dake kanta dan ji takeyi sun mata nauyi, takowa tayi tazo gabanshi tana mishi wani mugun kallo tace "Kace meye?, Aure?, Idrees ashe ko lallai zaka tafka babban kuskure na rayuwanka da baka taba yi ba wlhy, tun wuri ka gyara maganarka, kai d'in banza har ka isa tozartani kayi min kishiya?, wlhy Allah baka isa ba, bamu gaji ayi mana kishiya ba, You had better  take back your words tun muna mu biyu da kai kamin duniya ta jimu, kai ka ma isa kayi aure, toh duk munafikan da suka saka yi dan ganin bayana sunyi kad'an, Ka koma kace musu ta Allah ba tasu ba ni nafi karfinsu, ai babu mai yimin wannan tijarar ni nasani inba wannan tsohuwar da ka ajiye can gida ba", Tasss ya d'auketa da mari da yasa hawayen dake idonta ya shiga zubowa, mik'ewaKame tayi cikin zafin rai ta cakumo rigarshi tana "Wlhy sai kasan ka mareni, munafiki kawai maci amana, azzalumi, wlhy ba ni ka wulakanta ba sai tsohuwar banzar da ko tafiya batayi daka ajiye a gida, kwace rigarsa da ta cukwuikuye yayi daga hannunta snn ya kara mata wasu lafiyayyun marin, cikeda fushi ya shiga bugunta ko ta ina, duka yakeyi tana ihu tana zage_zage, duka yayi mata sosai har saida yaga ta jikata snn ya jefar da ita yayi yace "Keh kinyi kad'an, nan gaba koda wasa kika kuma zagar min Family sai nasa kinyi regretting, keh d'in har wata matar kirki ce da baza ayiwa kishiya ba?, mey kika iya a auren da har zai hanani yi miki kishiya kullum in kika fice kika bar gari sai lokacin da kika ga dama kike dawowa, wane mijin ne zai yadda matarsa take irin wannan shashancin, Y'ay'an da kika haifa da kansu basu san dad'in uwarsu ba, basu taba samun time d'inki, I have finally made my decision, aure ne nan da sati biyu zanyi shi" ya tsallaketa yayi ficewarsa daga d'akin amma har lokacin bakinta bai mutu ba sai zazzaga rashin mutunci takeyi, da k'yar ta iya samu ta mik'e ta janyo jakarta ta ciro wayarta daga ciki, tana kuka ta shiga neman layin wayar Mummy, bugu d'aya ta d'aga daga d'aya b'angaren tace "Wai uwar mey ya miki da ya uzzura miki da dawowa, jarababbe", Jainaba ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Nikam na shiga uku, Yaya kasheni yakeson yi", Mummy tace "Kasheki? Dan uwarsa shi ya haifake da zai kasheki, shege matsiyaci", Jainaba na sheshek'a tace "Yaya wai aure zaiyi shine ya kirani harda kayan fad'ar kishiya", Mummy ta buga k'irji ta miqe tsaye tace "Ni Zuwaira, Jainab Bakal Abuki, da hankalinki kike kiramin mijinki aure zaiyi?", Jainaba na kuka ta gama fayyacewa Mummy gaskiya da karyar abinda ya faru, Mum tasa salati, nan ta rarrashi Jainaba akan zasu nemo maganin matsalar snn suyi maganinshi, daga nn sukaci gaba da zaginshi da yadda za aci uban nashi daga nan sukayi sallama




💖💝BATUUL💖💝Where stories live. Discover now