*RA'AYI*
'''Na Safiyya'''*11*
"Zulfa, al'amarin yawon bin club d'ina destiny ne kuma Allah ya iyakance min shi dan haka kidaina kirana da 'yar nanaye sabida kalmar tana k'onamin zuciya in kuma kink'i to lallai matakin da zan d'auka akai bazai yi miki dad'i ba."
"Kin dad'e baki d'auki matakin ba kuma kisani banyi farin ciki da barinki zuwa club ba dan ni naso naga tsarabar jiki a gidan, kinga ansamu ribar yawo kenan"
"To na Allah banaki ba, banza wacce alkhairi yayi nisa da ita, tsakani na dake Allah ya isa, kuma kamar su Abba da Modibbo sunji halin da kike ciki, dan wannan karan bazanyi shiruba ko dan gudun bala'in da kike jawoma kanki kada yazo ya shafemu muna zaman zamanmu."
"Kifad'a masu ince tare mukeyi haka a shirye nake nima na sanar dasu yaron da kike tare dashi a club kuka had'u sannan bin maza yake kaiki club, kinga kome za'ayimin tare za'ayi mana".
"Ohk k'iyayyar da kike yi min ashe har ya kai kiyimin sharri da k'azafi irin haka?, tam yayi miki kyau amma ki sani ina da hujja mai k'arki akanki kuma wannan takardan da kikazomin dashi taneman inshiga k'ungiyarku ta lesbian itama zan nuna duk amatsayin hujjata haka zalika Zaheeda tana nan duk cikin hujojina ga kuma su Zubaida da Zeenat duk nasan suna da abin fad'a in maganar ta isa Modibbo's place, dan haka muzuba u will see who is the winner between me and u."
"Am Zarah bani paper, nabar zancen k'ungiyar dama nasan bazaki amince ba Darling Deena ce ta matsa min akan tana sonki in gayyato mata ke amma Allah bada san raina hakan tafarufa kuma dan Allah ki rufamin asiri kibar batun sanar dasu Abba, insha Allahu zan daina wannan rayuwar nan bada jimawa ba."
"Ya ilahi!!! Wato bama kishirya barinta ba, to Allah ya shiryaki cikin gaggawa, ita kuma Deena take ko wa kice mata tabi duniya a sannu mutuwa zuwa takeyi cikin rashin tsanmani".
"Nidai kice kinfasa sanar da su Abba inji." Ta furta cikin son watsar da zancen.
"Zulfa kitubama Allah tun kafin lokaci ya k'ure miki, wannan watsaststen rayuwa da kike ciki ba abu mai kyau ba ce, kiyiwa kanki fad'a tun kafin danasani ta riskeki kuma ki dage da rok'on yafiyar mai duka akan kurakuren da kika aikata, ki rabu k'awayen banza, ki maida hankali a ibadarki, Allah zai taimakeki tare da baki kariya akan shaid'anun aminai, ki yawaita zikirin Halaula...... Safe da marece sau 10, Allah zai tsare miki farjinki daga aikata alfasha."
"Uhmm ya Sayyada jazakillah, zan duba zatukanki ingani amma ni dai kimin alk'awarin kinbar zancen fad'awa su Abba dan shine abinda nafi buk'ata dake bawai wannan wa'azin ba."
"Lahaulah fi sha'atullah!! Zulfa!!! Anya umma ce ta haifeki ba sanja mata ke akayi ba a hispital?, inaga ked'in jinin iblis ne aka misanya mata bata Sani ba".
"Tabbas zancen ki hak'k'un dan da alama tayi kama da shaid'anu."
Muryan Ahmad yayi masu bazata, a kid'ime suke kallonsa tare da ja baya dan tabbas ba makawa yagamajin dukkanin zantukansu.
Ko kafin su ankara ya d'auke Zulfa'a da lafiyayyan mari left and right, ya kuma sa k'afa yayi ball da ita tayi mugun buguwa da bedside drawer, ta saki k'ara, ya zare belt d'insa yasoma zuba mata tana ta tsala ihu.
"Close the door." Ya umurci Zarah.
Jikinta na rawa ta aikata.
Yayiwa Zulfa'a lis, Zarah na gefe sai kuka takeyi tare da rok'onsa da yayi hak'uri hakanan kada ya halakata yazo yana da yasani.
"Wallahi ko na kashe wannan bazan tab'ayin danasani ba dan ire irensu a doron k'asa bala'i da masifa ne!!." Ya furta cikin tsawa.
"Neman mata azuri'ar mu, wa'iyazibillah, Allah ka kawo mana d'auki."

ESTÁS LEYENDO
RA'AYI
Romance"Mitchew!!" taja tsaki "Meke damuna ne ni ZARAH?' Ya Allah ka kawomin dauki alfarmar Annabin farko da k'arshe Amin.