*_Ummuh Hairan ce_*
_*Wattpad-realfauzahtasiu*_
🅿️1️⃣⏩2️⃣
_Part 2 na kudine ki biya ta wannan account din 0255526235 GTB ko Kati MTN ta wannan number 09013718241 or VTU ta 09031307566_
Miqewa sukayi dukkansu a sanyaye Suby tana sare hawayenta tace “bantabajin lbrn da yake tabamin zuciya kamar naki ba Zuhurah Allah yasa baki nemi saki gurin Alh Lukman ba nikam cikin su biyu bansan wanda yafi sonki ba" share hawayenta tayi da tisue tana me amsa Kiran da mijinta yakeyi Mata ta fita a hanzarce ta isheshi a qofar dakin baccinsu yanata huci gabanta ya fadi ta tsugunna tace “Allah yasa ba laifi nayi ba?"
Tsawa ya daka Mata yace “uban laifi kikayi yar rainin hankali kinsan banason jallop shine kikayimin kewai yaushe Zaki zama cikakkiyar mace me nutsuwa ne?" A sanyaye ta dago tace “Amma abban Husnah iyakar zamana dakai baka taba cemin bakason jallop ba sai yau...." Daga Mata hannu yayi yace “banson dogon surutu kije kiyimin faten dankali tunda ke qwaqwalwar kifi gareki baki gane daidai da rashin daidai harsai an fada miki Koda yake dama masans sunce qwaqwalwa da hangen nesa yana gurin mace me haihuwa Amma juya sai kayi da gaske....."Miqewa tayi a salube zuciyarta na tafasa ta dubesa tace “Amma dai kasan cewa juya bata batan wata balle har tayi bari ni Ina haihuwa Kuma inasa ran zan Haifa Ahmad tunda qwan yana shiga cikin mahaifa rashin kulawarka ne yake lalatashi"
Wani uban tsaki yaja yayi shigewarsa daki hakanan 11:30pm ta shiga kitchen tayi masa jallop din dankalin turawan duk da yace bayason jallop din shinkafa Amma yace ayi masa na dankali, tana gamawa ta zuba masa a flat ta dauka ta nufi dakin nasa ta tura da sallamarta yana kishingide yana wayarsa da budurwarsa ta ajiye ta miqe zata tafi ya riqo hannunta yajanyota jikinsa tare da cewa da budurwar.“Bye my Heart insha Allahu gobe da wuri zasuzo naje malumfashi nayi mgn da Hajiya" qit ya kashe wayar ya birkitata qasa ya haye samanta ta rintse idonta zuciyarta na tafasa tana maimata kalmar Innanillahi wa Inna ilaihirraji'un da haka ta samu salama ya dora bakinsa saman nata wasu hawaye masu dumi suka zubo Mata a ranta tana cewa “qaddara ta riga fata amma Ahmad Bai dace da tsarin rayuwata ba" tuhumar kanta takeyi mema yasa ta zabeshi bayan barinta hannun Alh Lukman? Meye yasa taqi yarda ta komawa Yaya Noor Kuma taqi aminta ta koma gdan Lukman? Meye yasa kishi ya hanata zabawa rayuwarta makomar data dace da ita?.
Da wannan tunanin taji yana qoqarin janye doguwar rigar jikinta ta ture hannunsa ya galla mata harara yace “banson iskanci ba zaman dadiro mukeba Kuma ba kyauta kike bani ba Saida na biya sadaki sannan ya zama mallakina" daga haka ya sutale wandonsa ya zare Mata rigar tana hawaye tana qara tuhumar kanta wanne irin miji take aurene da a wannan zamanin ya kasa sanin mubudan kunna mace shidai kawai yayi Mata hawan qawara buqatarsa ta biya shikenan,
Rintse idonta tayi lkcn da yake tura Mata dick dinsa tanajin wani Abu yana taso mata ta qasan zuciyarta, tabbas don ta gaji da sabawa ubangiji ne da tuni ta rabu da Ahmad Koda kuwa shine qarshen mijinta na duniya,Cikin minti uku yayi facal² dinsa ya tashi yana nishi ya dubeta yayi murmushi yace “kinada dadi shiyasa naqi rabuwa dake duk da halayenki basuyimin ba ni cikin halayenki mafi Muni dana tsana shine neman maza gashinan duk sun qarar Miki da ni'imar jikinki daqyar nake shigarki" karona uku kenan daya furta Mata wannan kalma daga shekaran jiyan zuwa yau.
Binsa tayi da idanunta daya tsike yama daina zubar da hawaye sai qunar zuciya a fili tace “Allah kanaji kana gani kafi kowa sanin abinda ke binne a qarqashin qasa da wanda yake sararin samaniya Allah ka sakamin ka wankeni daga wannan qazafin da wannan bawa naka yakemi...."
Dauketa yayi da mari jikinsa na bari ya zare belt ya fara jibgarta ta miqe da sauri ta fada bathroom ta datse tana haki ya kuwa dosa bala'i yana cewa “kajimin shegiyar yarinya ni zaki hada da Allah akan abinda na kamaki dumu dumu to mu zuba ni dake dan uwarki zanga Wanda ya tsaya Miki a garinnan qara ma zan shigar dake da iyayenki akan Abu uku na farko sun auramin ke bayan sunsan baqya haihuwa na biyu kinzo kin rabani da matata uwar yayana na uku Kuma kina neman maza da aurena akanki Kuma ubanki ne ya daure miki gindi tunda har yana da bakin cewa shi babu ruwansa da abinda ya shafemu domin bashi ya hadamu ba....."Yaka ya rinqa bala'i yana zage zage tanajinsa bawai don tanajin tsoron dukan da zaiyi Mata ba aa saidon gudun abin kunya yasata yin shiru saboda arziqin Suby da take gidan, ranar kwana yayi yana masifa sai gefin asuba sannan ya fice ya tafi masallaci hakan ya bata damar dauro alwala ta fito tayi sallah ta kwanta tana tausar zuciyarta da addu'o'i bayan tayi azkar bai dawo gdanba sai bakwai yana zuwa ko kallonta baiyi ba yasa kayansa ya fice daga gdan ta sauke ajiyar zuciya tare da miqewa ta nufi kitchen domin sallamar baquwarta.
Tea ta dafa musu ta soyansu dankali da qwai ta dauka takai Mata ta tararta tana shafa mai suka gaisa sannan suka fara break Suby ta dubeta tace “kayy mijin nan naki masifaffene Zuhurah jiya inajinshi yanata masifa wai meye ya faru ne?" Numfashi ta sauke tace “ki share kawai Suby" daga haka bata Kuma cewa komai ba ta miqe zata fita Suby tace “na matsu naji qarshen wannan sarqaqqen labarin naki Zuhurah don Allah kada kijamin rai" murmushin yaqe tayi tace “zan dan gyara gdanne sai mu zauna"Tare sukayi aikin gdan bayan sun gama sukayi wanka suka zauna Suby ta dubi Zuhurah tace “nidai ina roqonki kici gaba na matsu naji meye ya rabaki da Lukman har kika fado hannun wannan mara sanin darajar taki" daga Mata hannu tayi tace “bari Suby daina tabamin miji don Allah baya ta wucce yanzu ake zance" dagants hannu tayi alamun ban hqr tace tuba nakeyi me miji cigaba Ina sauraron ki"
Qasa tayi da kanta taci gaba da cewa
“Wadannan kalamai na Alh Lukman sai suka daskarar dani duk da kasancewar suna tasiri a jikina amma soyyayar taga gurin ruhina Suby haka mukaci gaba da rayuwa da Alh Lukman banida matsalar komai duk wayewar garin duniya kudin cefanena ma abin zance ne duk da babu ko magi ds nake siye komai akwai cikin lkcn nashiga tashin hankali fiye da qima saboda jarabar Alh Lukman ta girmi tunani na nikuma banajin komai ina yanayi bana samun gamsuwar ko kadan A dare saiya kusanceni sau biyar nakanyi kuka har nasara hawayen matsewa.
Muna wannan zaman dashi gefe yanaci gaba da koyamin wasan Polo har takai nima na zama wata tsiya a duniyar wasan Polo cikin watanni biyar din da nakasa mantawa dasu cikin rayuwata bawai mantawa nayi da rayuwata ba aa qoqarin tallafar qaddarata nakeyi tazomin daidai da bugun numfashina ma'ana so nake na gogews kaina tunanin barin Alh Lukman saboda fahimtar da nayi cewa zuciyarsa ta ta'allaqa ne ga tamu duk maganar duniya idan zaiyi Fatima Mardiyyah wannan abun yasani jin inason na hqr na rayu dashi iyakar abinda Allah ya hukuntamin.Amma fah kullum kwana nake Ina kuka tare da roqon Allah ya ciremin soyayyar Yaya yasamin ta mijina saidai hakan ya faskara abin ruruwa yake kamar wutar daji gefe Kuma ga kishiyata Mardiyyah ni lamarinta har mamaki yake bani kamar babu zuciya a jikinta kullum mukayi waya roqona takeyi na zauna dasu da zuciya daya suna sona Kuma suna fatan na Haifa musu yaran da zamuyi alfahari dasu baki daya.
Watana na bakwai kullum zan kira wayar Aunty Naja'atu duk da tayi aure bana qasar Ina Sweden da mijina akayi bikin ta gurinta nakejin lbrn Yaya Noor saboda Alh Lukman yacemin bazai yanke zumuncina dashi ba Amma idan wata mgn bayan gaisuwar zumunci ta shiga tsakanina da Yaya Noor to be yafemin ba, wannan dalilin yasa na dains kiransa shikam dama fushi yakeyi dani akan na karya masa alqawarinsa nan take fadamin ai yayi aure ya auri Zaliha yar abokin Alh Sadiqu mahaifinsa.Wayyoh ranan na tabbatarwa kaina Yaya Noor yayimin nisa ranar da zazzabi na kwana Alh Lukman ya gigice cikin tashin hankali da safe ganin Ina sumammaki ya daukeni sai asibiti dama lkcn muna Cairo ne muna zuwa suka fara bincikena abin ta'ajibi da rabo saiga bullar ciki na watanni biyu a jikina sannan da hauhawar jini me tsanani.
Allah Sarki bawan Allah sheksrarsu 17 da aure ko batan wata sister bata tabayi ba aikuwa kamar ya hadiyeni ya rasa inda zai sani saboda murna nikam banmasan wanne yanayi nake ciki ba zuciyata tana rayamin ban haihu da Yaya Noor ba zan haihu da wani daban, haka nake danne zuciyata da addu'o'i muka koma masaukinmu nan yashiga yayatawa duniya cewa matarsa tanada juna biyu kafin kace meye wannan abokansa na qasar sun cika masaukinmu sunata yimin kyaututtuka itama Mardiyyah murna a gurinta baa cewa komai sai nan nan takeyi dani Suby tundaga wannan rana banqara ko dauko ruwa a freegde ba dana motsa Sister zatace me nakeso haka shima, Amma nifa ba burgeni sukeyi ba,
Daga Cairo Sai muka Nufi Germany zasu buga wani wasa na qasa da qasa gida gudane damu a Germany dama tun a Cairo sister ta yafemin kwana a cewarta daganan har na haihu tabarmin shi nikam banji dadin hakan ba don ya addabeni, satinmu biyu a Germany na fara ciwon ciki me azabar masifa Sister tasa driver yakaimu asibiti saboda ranar Shi yana filin Polo suna atisaye muna zuwa suka shigar dani wani daki suka dubani sosai suka fito sukace dole suna buqatar mijina.......
Please
Comments
Share
Vote~Ummuh Hairan~
