RUWAN JIRA.......

755 27 0
                                    

*RUWAN JIRA....BOOK 2*

*_Ummuh Hairan_*

*_Wattpad-realfauzahtasiu_*

🅿️1️⃣5️⃣▶️1️⃣6️⃣

_Part 2 na kudine ki biya tanan VIP 500 regular 200, account 0255526235 Fauziyya Tasi'u Umar GTB ko Kati MTN ta nan 09013718241 or VTU ta 09031307566 wadanda suke Niger zasu tuntubi wannan number ta WhatsApp +227 84 50 64 76_

Ranar wayana a rufe ta kwana washe gari na yini Ina juyi a kewar yayana tafi komai damuna na dauki waya na Kira number Mardiyyah ta 9ja abin mamaki a rufe hankalina ya tashi na katse na Kira ta Alh Lukman shima a kashe wlh bansan sanda na kurma ihu ba shikenan ya debemin yayana yabar qasar dasu banida ikon ganinsu ko jinsu, daqyar Minaye me aikina ta bani baki kafin na iya tsayar da kukana Ina fadin Yaya Noor ka cuceni kasa na rabu da mijina na fusata iyayena kaqi aurena qarshe ka maye gurbina da wata,
Wannan abu har ciwo yasamin da yamma su Ahmad sukazo Ina kwance a daki Minaye taje ta fadamin baqina na jiya sun dawo daqyar na miqe nayi wanka na zura doguwar riga na fito suna harabar gidanna fita muka gaisa Kabir yanata zubamin surutu da bayanin yanda abokinsa ya susuce daga ganina shikuma ya zubamin ido duk dagowar da zanyi muna hada ido can yaja numfashi ya matso ya sanya hannu ya dago fuskata sai naga ya saki a firgice yace "subhanallahi kuka Fatima why?" Saurin share hawayena nayi na miqe zan tafi daidai lkcn aka bude get na zubawa me shigowar ido gabana yana faduwa shima ni yake kallo tundaga get din yana sabe da jakarsa ya tsaya nesa damu yana qanqantar da idonsa da alamun bala'i zaiyi nikuwa na kawar dakai da niyyar tura masa baqin ciki na kalli Ahmad nayi murmushi nace "kada kadamu kawai Ina tuna wani abune daya wucc..."

Jinayi an kamo hannuna na dago da sauri saboda hucinsa da naji tare da ja da baya ya matso yace "su waye wadannan Zuhurah?" Yanda yayi mgnr da qaraji yasa hanjin cikina kadawa Amma saina aro juriya nasawa kaina nace "ina ruwanka dako suwaye Nuraddeen Ina a gidana ka tarar dasu baa gidanka ba?" Sakin hanuna yayi yaja da baya da sauri yana cije lebansa jikinsa yana rawa na zaci barin gidan zaiyi kamar yanda ya saba idan ta tarar da Alh Lukman yazo gurin yaransa a baya, sabanin haka sai naga ya shiga parlour naja dogon tsaki tare da kallon Ahmad nace "duk naji kalamanka Kuma na amince matarka da yarinyarka ba matsalata bace kamar yanda na fada maka niba budurwa bace nayi aure har biyu wannan daya shigo yanzun yayana ne Kuma mijina na farko da qaddara ta rabamu munason juna sai mijina na biyu Wanda shima yana Sona muka rabu Kuma shine uban yayana biyu Aadeel da Aadeeha twins ne Ahmad idan har da gaske kakeyi nabaka sati daya ka tura iyayenka Kano a daura aurena dakai....."

Wani ihu Ahmad yayi yayiwa Allah godiya yace "kamar kinsan a matse nake Salma gaf take da qara haihuwa...." Shiru naji yayi batare daya qarasa zancen ba na dubeshi shima Kabir shi yake kallo yace "yadai angon bazata?" gwauron numfashi ya aje yace "akwai wani hanzari Fatima banida gida a Kano saidai haya nakeyi kasancewar acan nake aiki a wani asibitin gwamnati Amma iyalina tana Malumfashi sannan anan a hostel nake zaune abinka da qaramin ma'aikaci" murmushi nayi nace "duk ba matsala bace indai da gasken kakeyi nan gdana ne sai mu zauna kafin lkcn da zangama karatuna mu koma Kano gabadaya shima kanon Allah zai kawo mafita" gdy yayimin nayi murmushi nace "ku fara bincike daga yau" Ina fadin haka na shige ciki Ahmad yabini da kallon mamaki shiga nayi na mayar da qofar na rufe zuciyata tanason taje taji dame Yaya Noor yazo, ilai kuwa Ina shiga ya shaqoni jikinsa na tsuma yace.
"Ubanme ya hadaki da wadannan yan takife din Zuhurah me sukazo yi Miki gidannan?" Zame hannunsa nayi nayi murmushin yaqe nace "inma yan tabare ne nidai su na zabo Kuma shine mijin da zan aur... "

Wani gigitaccen mari Yaya ya daukeni dashi na dafe kuncina da sauri ya hankadani kan kujera yana nunani da yatsa yace "saboda ke na yanke igiyoyin zumunci dana mutunci da yawa Zuhurah saboda ke nayi sake saken aure Kuma nake kanyi Zuhurah meye yasa zakiyimin haka na saki Hauwa sabida tace batasonki Tsoho yace bazan aureki ba saidai na auri Uzaira nabarsu sun daura naje har Rano gaban ubanta na bata saki uku to meye yasa ke zakiyimin haka wlh Koda tsoho bazai janye furucinsa ba to nima bazan janye qudurina ba zanci gaba da rayuwa babu aure daganan har zuwa lkcn da ajali zai riskeshi toke meye yasa bazakiyimin wannan halaccin ki tsaya kiji abinda zance Miki ba zaki zabi hadani da wani kina tunanin idan rabon twins yasa na hqr na qyalewa Lukman ke zan qara hqr na barwa wani dan iska kene Zuhurah...."

RUWAN JIRA......Where stories live. Discover now