Chapter 25

344 13 0
                                    

*RUWAIDAH*

'''Love And Romantinc Story💋'''

*Salon Na Daban Ne.👌🏻*

~*Free Book*~

            _*NA*_
        
_Real Ladingo Oummu Fareesa😘_
 
*Ƴar Mutan  Niger🤙🏻*

'''Wattpad@Rahamaummufareesa'''

_*🕌JUMMA'AT MUBARAK🕌 YA ALLAH KA SADAMU DA ALKHAIRIN DAKE CIKIN WANNAN RANAN, SHARRIN DAKE CIKINTA KUMA ALLAH KA KAREMU DASHI, DAN HASKEN ANNABI MUHAMMAD SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM.*_

*Bismillahir Rahmanir Raheem*


_*Chapter 25*_

Ɓangaransu Ruwaida kuwa tin ɓayan sallar la'asar suka shirya zasu tafi asibiti'n, Mummy ta tsayar dasu tana girkama Acp haɗadɗan girki da kanta, su tafi dashi, dole suka jira Ruwaida tabi Mummy kitchen tana kama mata, ba yadda batayi ba ta zauna taƙi dole tare sukeyin girkin.
                        Acp tin kan su Rahma su iso ya ƙira Dr Hanna, wacce anan hospital ɗin take, kasancewar su 2 masu duba family ɗinsu, ya sanar amaryasa na kan hanya aduba masa ita, batada lfy.     Su Rahma suna zuwa hospital ɗin, Dr Hanna ta shiga duba lafiyarta nan ta gano matsalarta, allura 2 ta mata ta rubuta mata maguguna.  Rahma ta marerece tana kallon Dr tace“Pls Dr karki cema Safwan ciwon marace, kice masa ciwon kaine, sai zazzaɓi amman naji dama sosai kinmin allura.   Ta ƙarashe mgnr tana ciza lips ɗinta.    Dr Hanna tayi murmushi tace.
                                   “Ok ba damuwa muje ya ganki a mayar dake, dan yace min na kaiki wajansa.” Rahma bata musaba cikie da kunya ta ɗaga kanta, Zainab tace“Aunty to ki daina langwaɓewa.    Hararata Rahma tayi ta saita nutsuwarta suka fito.     Kwance yake waya ahannunsa yana latsawa alamar ma wani abin yake bincikawa ta cikin wayar.    Musaddiq da Nadeer suna gefe suna hirasu, yana jinsu baice masu ƙalaba. 
                        Dr ta turo ƙofar suka shigo da sallama.   Su Musaddiq suka amsa, Rahma ta gashisu cikin girmamawa, suka amsa harda Zainab.   Abbaye ya waigo yana amsa sallamar, yana kallon Rahma ganin yanda idanunta suka faɗa, ahankali cikin nutsuwarta take takowa wajansa.   Idanunsa ya ɗauke daga kanta ya yamar kan Dr can ƙasan maƙoshi yace“Dr Hanna ya dai meke damunta?”  Rahma ta ƙaraso ta zauna saman kujera dab gadon tace“Ina yini.   Acp ya miƙe zaune ya ajiye wayar hannunsa yana kallonta yace“My dear ykk y jikin hope kinji sauƙi?”     Kai Rahma ta ɗaga cike da kunya.   Dr tace“Ciwon kaine da zazzaɓi amman taji sauƙi, ga takardar maganinta....”  Acp ya katseta yace“Pls ki bada a amso mata maganin nanɓcikin pharmacy, Sani dureba na jiransu ya maidasu gida.”  Dr ta fice tana girgiza kai.       Musaddiq da Nadeer sukace“Rahma sannu ALLAH baki lfy.    Ta amsa da “Ameen Ngd.    Zainab tace“Ya

Abbaye ni ko gaisuwata bazaka amsa ba ko?”  hannayensa ya haɗe yace“Kaina bisa wuyana.   Ya ƙarashe mgnr yana rankwafo da kansa dab da fuskar Rahma, har sunajin hucin junansu, ta runtse idanunta sbd wani irin masifaffan ƙamshinsa da ya sakar mata kasala.  Ɗan guntun murmushi yayi ya janye kansa yace“Amaryata Allah baki lfy.”  Zainab tace“Ameen.   Rahma dai kunya ta hanata mgn kanta aƙasa.
          Dr tana fita taba wata nurse ta amso magugunsn a nan cikin pharmacy, ta aiketa takai ma Acp.  Ana kawo maganin Rahma ta miƙe tana faɗin“Zamu wuce Allah ƙarama lfy.   Acp ya amsa da“Ameen Tnx My dear, kema Allah baki lfy.   Rahma batace kome ba Acp ya beƙama Zainab maganin aleda ba tare da ya buɗe ba, sukama su Musaddiq sallama suka fice.
            Acp ya kallesu yana shan kunu, suka bushe da dariya, ya taɓe baki ya koma ya kwanta baice masu ƙalaba, yana ji suna tsokarsa.   Suna fitowa compound ɗin asibiti'n suka nufi wajan Sani ya buɗe masu mota suka shiga yaja ya fice daga asibiti'n ahanya ne Mummy ta ƙirasa yazo maza yakai su Ruwaida hospital, sosai yay gudu cikin ƴan mintina ya ajiye su Rahma ƙofar gidansu, ya juya ya nufi unguwar ( *Millenion suit*)

RUWAIDAHWhere stories live. Discover now