NOT EDITED.
wasu irin hawayene suka ciko idanuwansa dasuka qanqance sbd yunwa da wahala dakuma fargaba,
kallon mutanen dake miqa masa hannu yake kamar wani wawa sbd tsanananin mamaki da farin cikin daya kasa gasgatawa yau NUR tazama tasa da sauri ya miqe yayiwa allah sujjada yatashi tareda rungume sufyaan daketa faman washe baki farin cikinsa baya misaltuwa.saida aka gama komai mutane suka watse suka sakeyiwa mal liman da baffa godiya sosai nan sufyaan yayiwa mal liman babbar kyautar kudi sosai sukai masa bankwana suka wuce sbd so suke su isa abuja da wuri,
gida suka nufa ahanya ya zare babbar rigar tareda zuba hannunsa a aljihu murmushi yake saki yana tafiya kwata kwata hankalinsa baya taredasu sufyaan da baffa shi wata duniyar tunanin dayake dabam,
sufyaan na lure dashi yasaki murmushin farin ciki yana girgiza kai tareda cigaba dayiwa baffa bayanin wucewa zasuyi yanxu.
kudinda yatanadar masa tun jiya ya ciro yabasa cikin girmamawa yace,
insha allah dakomai ya gama daidaituwa zasu sake dawowa sukawo gaisuwa.
godiya kawai baffan yayi tareda cewa,
bakomai allah dai yakawo fahimta acikin alamarin cikin sauqi.
amin''''sufyaan yace yana kallon gefen dawood da wani irin annuri ke fita fuskarsa baimasan mesuke cewaba.
suna isa gida cikin tsananin farin ciki inna halima tayi musu allah sanya alkhairi sufyaan ne kawai ya amsa dawood hankalinsa nakan qofar dakin datake yasan kuka takeyi kobaa fadaba.
ko dakuna basu shigaba sukace wucewa zasuyi,
inna halima tashiga dakin datake takalleta taga har lokacin ko wanka batayiba tana zaune yanda take tundazu harlokacin jikinta bai daina rawaba.
dafata inna tayi tareda yimata yar qaramar nasiha ta dagota daqyar suka fito tana fitowa idanuwanta suka sauka cikin nasa ta sunkuyar dakanta tareda dagawa baffa dake mata magana kai.
'yar nasiha baffan yayi mata tareda bawa dawood amanarta suka fito,
motarda sufyaan ya dauko musu tun jiya shata har qofar gidan ta qaraso suka shiga suka wuce hawayenta na saukowa ahankali na fargabar abunda zasuje sutarar.
sufyaan ne agaba itada dawood din abaya tunda tashiga ta juyar dakai gefe tareda rufe idanuwanta ahankali sbd ko jinsa zaune gefenta tsananta bugun zuciyarta yake bare ta iya kallon gefensa.
qura mata idanuwansa dasukayi laushi yayi cikeda wani irin farin ciki shikadai yasan irin rayuwar dayake musu tunanin shimfidawa kafin sudawo sbd bazai ta6a gangancin bari suje gida yanxuba a 6angale masa auren dako kwana daya baiyiba aduniya dan yasan sarai hakan zata iya faruwa takowane 6angare na mum dinsa kona su aleeya.
doguwar tafiya sukayi babu wanda yayi magana acikinsu basu iso abuja ba sai yamma sosai nan sufyaan yayiwa drivern magana kai tsaye ya nufi gidan maska dasu.
lokacinda suka isa gidan sosai taji habkalinta yatashi ta kalli dawood din da sauri ganin yaciro mukullin gidan inda suke aje spares cikin wata flower dake qofar shiga,
daure fuska yayi nantake yakoma dawood dinsa sbd karma tasamu fuskar jeho masa wani zancen,
ganin yanayin fuskarsa yasa ta sunkuyar dakai tareda rufe ido hawayen ciki suka sauko ta share ahankali,
suna shiga sufyaan yayi saurin shigewa bedroom daya yabarsu apalon.
kallonta yayi yaga yanda ta tsaya batada alamar motsawa ya matso ahankali yakamo hannunta yakaita har tsakiyar 'dayan bedroom din ya juyo yafito yakoma wanda sufyaan yake sbd duka gidan is two bedrooms flat ne,
![](https://img.wattpad.com/cover/158188301-288-k195557.jpg)