PAGE* 5⃣4⃣
Ahaka yarima yaje wajen aiki ammah kwata-kwata baida kuzari, Dr khalil shi kansa saida yalura da yanayin yarima,,,,,ko da yatambayesa abinda yake damunsa yarima banza yayi dashi yak'yale, kan dole Dr khalil yaja bakinsa yayi shuru dan ya san kome zaiyi toh bazai samu amsar tambayarsaba.
Zarah koda tashige bedbroom d'inta saman bed d'inta tafad'a tashiga tacigaba da kukanta wani irin son yarima ne yake fizgarta daga gefe guda kuma haushinsa takeji,,, ahaka tasha kukanta saida taji yunwa tana niyar yi mata illah sannan tamik'e taje wanko fuskarta tafita tad'auki coffeenta tasha.
Sumayya koda yarima yakoreta daga part d'insa bata wani damuba sosai cikin ranta cewa tayi na zan hanyar da zan 6ullo maka,,,,daga nan wucewa tayi tatafi turakar iyayenta.
Tana shiga a parlour ta tarar da sultana sadiya kishingid'e tsakiyan kuyanginta suna ta yi mata hidima, ganin sumayya yasa suka zube gabad'ayansu suna kwasar gaisu sumayya ko kallon inda suke batayiba ganin haka yasa cikin sauri suka ficce daga parlourn gudun kar suyi laifi.
Sultana sadiya tana ganin sumayya ta shigo nan tahad'e fuska babu alamun fara'a ko kad'an a tare da ita.
Sumayya jiki ba k'wari tazo tazauna gefenta ahankali tace ummana.
Sultana sadiya batare da ta kalletaba tace me yakawoki wajena.
Sumayya fashewa tayi da kuka tare da fad'awa jikin sultana sadiya, shuru sultana tayi tak'yaleta.
Cikin kuka sumayya tace ummah dan Allah kiyi hak'uri wlh na daina.
Sultana sadiya sai a lokacin ta kalleta tace sumayya kikyaleni kawai tunda bakyajjn magana kije kawai na sallamaki wajen wad'anda kike jin maganarsu.
Sumayya Cikin kuka tashiga girgiza kai ahankali tace ummah wlh ina jin maganarki akasine kawai aka samu kuma insha Allahu na daina bazan k'araba, dan Allah kiyafe min wlh duk na zubar da pills d'in.
Sultana sadiya cike da tausayin d'iyartata tashiga d'an bubbuga mata bayanta kad'an cikin sigar lallashi tace toh shikenan sumayya na hak'ura ammah dan Allah kidaina irin haka kinsan idan labari yajema su dada bazakiji da kyauba ke kinsan ko mahaifinki yaji sai kashinki ya bushe.
Sumayya share hawayen fuskarta tayi cikin jin dad'i tace insha Allahu ummah ba zan sakeba.
Murmushi sultana sadiya tayi tace yauwa d'iyata, yanzu sai kije kisamu kilallashi wanchan miskilin mijin naki ko shima ya safko, Allah yaimiki albarka.
Ameen ummana, insha Allahu zan k'ara bashi hak'uri....nan tazauna sukasha hira da ummah cike da jin dad'i sannan daga baya tayi mata sallama tafito tanufi turakarsu dada dan tagaisheta.
koda tashiga fuskarta d'auke da murmushi taduk'a tagaishe da dada,
Cikin jin dad'i dada ta amsa mata nan sumayya tazauna gefen dada tana murmushi tace 'yar tsohuwa me kika ajemin?
Ido dada tazuba mata tace me fa zan aje miki bayan gakinan kinyi 6ul-6ul da ke kin koma d'imemiya wai mi wanchan miskilin yake d'irka miki?
Dariya sumayya tayi tace wlh dada hutune kawai,,,dada cikin rashin yarda tace kodai mun samu k'aruwane?
Girgiza kai sumayya tayi tace wlh dada banda komai.
Rik'e ha6a dada tayi tace sumayya kodai zakije asibiti aduba lafiyanki, tunda shi wanchan miskilin bai damu da hakanba.
Dada na je ance lafiya ta lau fa kawai dai lokacine baiyiba.
Ajiyar zuciya dada tasafke sannan tace toh Allah yanuna mana lokacin, Allah yasa ina da rabon ganin d'an cikinki.