13

2.3K 82 3
                                    

page 1⃣3⃣


Abbah gyaran murya yayi sannan yace maganar barin gida duk bata tasoba a yanzu muma mungane kuskurenmu tabbas duk abinda mutum yashuka shi zai gir6a wlh banga laifinkuba tabbas bamu dace da mukasance iyayenkuba, Abbah girgiza kai yayi yace kaicona da nabari son abun duniya yarud'eni har nawatsar da tarbiyar yarana alhali ni iyayena bahaka sukayi min ba,  son zuciya da kwad'ayine suka ja mana dan Allah kuyi hak'uri da mummunar d'abi'ar da muka d'auraku akanta,  wannan ya zama darasi a garemu ayi hak'uri a yafi juna.

mama cikin kuka tace dan Allah kuyafe mana insha Allahu yanzu zamu gyara tsarin gidanmu da komai zakuyi alfahari da mu.

Zarah ce tace bakomai wlh mun yafe muku duniya da lahira muma kuyafe mana.
kallonta tamaida ga su Rauda da basu da niyar yin magana tace yaya Rauda dan Allah kuyafe ma su mama tunda sun gane kuskurensu.

Rauda da Aysha cikin kuka sukace shikenan mun yafe musu Allah yayafe mana gaba d'ayanmu.

gaba d'aya suka amsa da Ameen.

sannan Abbah yace toh Alhmdllh da Allah yataimakemu muka farka tun kafin lokaci yak'ure mana naji dad'in hakan, insha Allahu zanyi k'ok'ari duk wani hak'inku da yarataya kaina inga na safke muku shi, saidai matsala d'aya yanzu cikin da yake jikin Rauda bansan ya zamuyi da Shiba.

Mama ma tayi nisa sannan tace mezai hana azubar da shi?

Zarah da sauri tagirgiza kai tace a'a mama bai dace azubar da shi ba karfa mumanta shi fa d'an baida alhakin kowa sai ma su da yakeda alhaki akansu da suka samesa ba ta hanyar halak ba,  ga laifin zina ga na kisan kai ai k'ara tahak'ura tafauwala ma Allah lamurranta saboda Allah yana sane da halin da take ciki kuma komai rubutaccene ya riga ya tsara ma kowa yadda rayuwarsa zata kasance,  shin baku tsoron wajen zubar da cikin tarasa rayuwarta?  idan taje me zatace ma ubangijinta ranar gobe k'iyama?  Shin kunsan yadda rayuwa zata kasance a nan gaba ko kuna tunanin nan gaba zata k'ara haihuwa? yakamata mumik'a lamurranmu ga Allah ubangijinmu mucigaba da rok'onsa tare da neman gafararsa Allahu gafurur rahim ne.

Dukkansu jinjina kai sukayi alamun gamsuwa da bayanin Zarah, Abbah yace tabbas Zarah nagamsu da bayaninki Allah yayafe mana kuskurenmu wlh ke d'iyar kirkice, kekuma Rauda Allah yasafkeki lafiya.

Gaba d'ayansu sukace Ameen, mama tace Allah yayi muku albarka Allah yaraya mana ku.
cike da jin dad'i sukace Ameen mamanmu,
muma muna alfahari da ku Allah yabar mana ku.

daga nan suka shiga tsara yadda zasu tafiyar da rayuwarsu, Aysha da Rauda 'yan kud'in da suke hannunsune suka tattara suka ba iyayen nasu sukace asiyo kayan abinci,

tun daga ranar suka rabu da samarinsu  gidan yagyaru, inda Aysha takoma islamiyya suna zuwa tare da Zarah, Rauda kuma tacigaba da rainon cikinta, a gida Zarah takeyi masu k'arin karatunsu Rauda da Mama.

cikin ikon Allah Abbah yasamu d'an aikin da ake biyansa duk wata da taimakon Allah yake samu yana rik'e gidansa gwalgwadon k'arfinsa,

su kansu a yanzu suna jin dad'in sauyawar da suka samu ta rayuwa.

_______________

Yarima Suhail yau tunda yatashi jinsa yake wani iri ga tsananin buk'atar sumayya da yakeyi daurewa kawai yake tsawon wata biyu kenan rabonsa da ita.

yau bayan yadawo wajen aiki yayi wanka ya shirya cikin shigarsa ta alfarma fitowa yayi yanufi part d'in sumayya domin yau ji yake hak'urinsa ya k'are baya iya cigaba da daurewa


Yarima d'akinn sumayya yashiga lokacin sumayya tana zaune a parlour tsakiyar kuyanginta suna ta mata hidima.

ganinsa yasa dukansu suka zube suna kwasar gaisuwa yarima baibi ta kansuba yashige bedroom d'in sumayya, da harara sumayya tabisa sannan tamik'e tabi bayansa.

Yarima SuhailWhere stories live. Discover now