14

2.2K 87 2
                                    


page 1⃣4⃣

Zarah ko da tashiga gida d'akin mama tashiga ta tarar da mama tana linkin kaya ganin zarah yasa tasakarmata murmushi tare da cewa 'yan makaranta andawo?

zarah ma murmushi tayi tace eh mama dafatan mun sameki lafiya?

mama tace lafiya lau, nan zarah takama mata suka cigaba da linke kayan,  cike da nutsuwa zarah tad'auko kud'in tamik'a ma mama tace mama ga kud'in da kuka bani.

mama da mamaki take kallonta tace zarah ya haka?  ya naga kin maido kud'in?

murmushi zarah tayi tace  mama daman da naje inbiya shine akace malam bello ya biyamin kuma na kai masa kud'in yace bazai kar6aba shi dan Allah yayi min nayi-nayi yakar6a ammah ya k'i.

mama tace Allah sarki gaskiya yana d'awainiya dayawa mungode sosai Allah dai yabiyasa,  yanzu kud'in ki aje wajenki kinga sai kiyi anko d'in da su,

zarah tace toh mama nagode sosai Allah yak'ara girma da rufin asiri.

mama cike da jin dad'i tace Ameen 'yar albarka nidai fatana a kullum Allah yakawo muku mazaje nagari kuyi aure.

zarah dagudu taficce tabar d'akin cike da jin kunya,  mama dariya tayi sannan tacigaba da linkin da takeyi.


tun ana saura kwana hud'u ayi walimar aka bugo Invitation card aka gayyaci mutane da dama daga cikin wanda aka kaima katin gayyata har da maimartaba.


A gidansu zarah suma shirye-shirye suke daidai k'arfinsu,  Abbah bakin gwalgwado yasiyo mata abinda zata raba ma abokanta da 'yan uwa.

malam Bello ma ba'a barsa a bayaba domin carton din lemu  yasiyamata yakai mata dakyar yasamu zarah takar6a.

ana gobe za'ayi walimar gidansu zarah tun dare aka fara shirye-shiryen abinda za'a raba ma mutanen da suka gayyata kasancewar da k'arfe goma za'ayi walimar.
_______________

yarima tun daga lokacin yafita harkar sumayya ganin tana neman rainasa akan hak'insa yasa yajefar da ita gefe yacigaba da hidimarsa,  sumayya tun tana daurewa itama taji bata iya daurewa.

yau ma kwance take tana ta juyi saman makeken gadonta tsaki kawai takeja tana neman mafita,  chan tayi nisa tace daman ace zinat zatazo da nad'an samu sauk'in abinda nakeji,  ammah bari inkirata ko ta flight ce tabiyo tazo yau, wayarta tajawo takira zinat ammah kashe wayartake, 

tsaki sumayya taja tare da wullar da wayar tace matsalata da ita kenan ayita nemanta ba'a samu.


Sultana Bilkisu ce zaune a turakarta tana kallon wata drama a faskekiyar TV d'in da take manne a bangon d'akin, gefenta kuyangine zaune k'asa suna jiran jin umurni daga wajen mai d'akintasu.

Sultan Ahmad ne yashigo da sallamarsa dasauri duk suka zube suna kwasar gaisuwa,  cike da fara'a ya amsa musu,  nan suka tashi suka ficce daga d'akin ahankali yataka yaje inda matarsa take zaune tazuba masa ido fuskarta d'auke da murmushi,

shima murmushin yayi tare da zama kusa da ita, rik'o hannunsa sultana bilkisu tayi cike da kulawa tace daddynsu suhail barka da dawowa muje daga ciki.

sultan Ahmad tallabo fuskarta yayi yace sultana ai banje ko'inaba yau ina fada daga chan naje wajen dada munata shan hira.

Sultana Bilkisu tace Allah sarki, ya wajen memartaba duk kwanan nan bamu gaisa da shiba duk lokacin da zanje gaishesa toh yana chan fada.

sultan Ahmad yace lafiya lou,  daman nima sawa yayi aka kirani yayi min magana akan wata walima da aka gayyacesa shine yace ni inwakilcesa inje tunda gobene zaya fita, kuma babu dad'i ace babu Wanda yaje daga wajensa.

Yarima SuhailWhere stories live. Discover now