22

2.5K 100 3
                                    

PAGE* 2⃣2⃣

Abbah gyara gidansa yayi sosai akayi masa fenti yacanza ma mama kujerun d'akinta,  d'inkuna kala ukku-ukku yayi ma su mama.

khairy ko da tazo taga zarah rikicewa tayi cike da murna tace sis anya kuwa kece ba canza mana wata akayiba mai kama da ke?

murmushi zarah tayi tace toh indai ana canza mutum toh nima an canzani,

khairy tace wlh kuwa dan ma bakiga yadda kika koma wata 'yar gayuba,  ke ni ya maganar rabon invitation card gashi saura kwana biyu bikki ammah ba Wanda muka gayyata.

ta6e baki zarah tayi tace ba wanda zan gayyata domin ba abinda zanyi ayi bikkin kawai a haka.

khairy rik'e baki tayi tace kai zarah ammah dai bakida mutunci yanzu saboda Allah bazaki gayyaci kowaba?  gaskiya bai daceba ace kamarki zaki auri yarima guda ammah ba ayi wani shagaliba,

zarah cikin rashin damuwa tace ba fa zanyiba kema kinsan auren nan zanyisane kawai ba dan ina soba.

zaro ido khairy tayi tace zarah kar dai kice min har yanzu baki daina son malam bello ba? yarima fa yafisa komai.

murmushin takaici zarah tayi tace har yau har gobe ina son malam bello,  saidai idan nayi aurene zan daure inga na nisantar da zuciyata daga tunaninsa gudun kar injefa kaina ga halaka.

dariya khairy tayi tace kin dai karanta a islamiyya kuma kinsan babu kyau ehe.
ke wlh yaci ace kin cire son malam bello a ranki kifad'a sabuwar soyayya.

murmushin takaici zarah tayi tace kar fa kimance da tsohuwar zuma ake magani.

dariya khairy tayi tace injiwa?  ai itama sabuwar zuman tana magani wani lokacin ma tafi wata tsohuwar, zamu dai zuba ido mugani.


su Hajiya sa'adatu sune ummi tasa sukaje sukayi jeran zarah, part d'aya aka fitar mata dashi daga cikin gidan yarima suhail,
d'akine mai d'aukeda parlour nd 2 bedrooms sai kitchen, kaya aka zuba mata na gani na fad'a a duka bedrooms d'inta sannan aka tsara mata parlourn ta yayi gwanin kyau,  kitchen d'inta cika mata shi akayi da kaya, antsara ma zarah part d'inta sosai kamar na wata d'iyar wani attajirin mutum.

Abban sumayya ma canza ma d'iyar tasa kayan d'aki yayi masu kyau da tsada,  sumayya taji dad'i sosai sai a lokacin ta safko daga fushin da take da mahaifinta akan auren da yaje yanemo ma yarima.



ana gobe bikki sultana bilkisu ta aiko da mota akazo aka d'auki zarah aka kaita wani hadad'en shagon gyaran jiki wanda sai amaren da suka amsa sunansu suke zuwa.

saloon akayi mata sannan aka zizira mata k'unshinta tayi kyau sosai.

gidan sarautar hidima ake ta gani ta fad'a ko da kowa 6oye murnarsa yake a ciki,  ammah sumayya da mahaifiyarta  a fili suke nuna basason auren.

gimbiya rahma ita take zuwa tana kwantar ma da sumayya hankali tun da bikkin ya matso kasancewar itama ba'a son ranta yayan nata zai k'ara aureba saboda tana ji da sumayya sosai tun k'uriciyarsu suke abota,  taso ace ummi ta hanasa yak'ara auren ammah ummi tace babu ruwanta ita taje ta samesa tayi masa magana,  jin haka yasa taja bakinta tayi shuru dan tasan bama zata iya tunkarar yarima da maganar ba.

________________

zarah bayan angama mata gyara around 3:30pm aka maidota gida, mamakine yacikata ganin mutane da suke shiga gidansu, kanta bai ida d'aurewaba saida tashiga cikin gida taga kowa ya shirya, Yaya rauda ce tafara hango zarah tace yauwa ga ma tanan ta dawo.

dasauri khairy da Aysha suka zo wajenta sukace tun d'azun muna ta jiranki please kizo kishirya lokaci yana k'urewa, zarah cike da mamaki tace ban fahimcekuba me zanyi?

Yarima SuhailWhere stories live. Discover now