PAGE* 2⃣4⃣
Yarima ganin zarah tana shirin wucewa part d'inta yasa yace suje part d'insa yanason ganinta, zarah bata musaba tabi bayansa dan bata iya musama yarima saboda girmansa da take gani.
ko da suka shiga saman cushin yarima yazauna, zarah har zata zauna k'asa yace tazauna saman cushin tunda suka zauna d'akin yad'au shuru.
yarima kiran sumayya yayi tana d'auka cike da jin haushi yace kinsan dai bana jira kuma baki isa inzauna ina jirankiba.
tsaki sumayya taja tace ai ganinan a hanya.
bayan minti biyu saiga sumayya tashigo fuskarta babu alamun fara'a ganin zarah yasa taja bakin k'ofa tatsaya, dasauri zarah tamik'e tad'an russuna tace Aunty barka,
wata uwar harara gimbiya sumayya tawurga mata tare da jan tsoki, tace Auntyn munafunci? kece kika auran min miji ko? lallai natayaki murna tak'arashe maganar tare da yin k'wafa
jikin zarah duk sai yayi sanyi.
yarima da yake dannar waya yana saurarensu batare da yakallesuba yace ma gimbiya sumayya ai saikizo kizauna kin wani yi ma mutane tsaye,
sumayya tana hararar zarah tatako cike da isa tazauna saman kujerar da yarima yake zaune, zarah ma jiki ba k'wari tazauna inda take tare da saddar da kanta k'asa.
yarima shuru yayi yana dannar wayarsa baice komaiba saida akayi kusan minti ukku,
sumayya ta k'ule kallonsa tayi tace haba yarima ya zakayi shuru kabarni a zaune.
banza yarima yayi da ita saida yagama abinda yake sannan yad'ago kai yakallesu d'aya bayan d'aya tare da gyaran murya kamar bayason yin magana yace toh Alhmdllh ba akan komai natarakuba sai dan infad'a muku dokokina domin duk wadda takeson zama da ni dole tabisu, kallon sumayya yayi da taci face yace ke sumayya kece babba dan haka kija girmanki banason fitina ko tashin hankali, sumayya cike da masifa tabud'e baki zatayi magana, yarima hannu yad'aga mata yace kar kikuskura, kin san wanene ni idan ina magana ba'a tsinkemin.
sannan yamaida kallonsa ga zarah da take wasa da yatsun hannunta yace ke kuma kece k'arama dan haka dole kibata girmanta sannan kizauna da ita lafiya kar kikuskura inji kinyi mata rashin kunya, zarah shuru tayi batace komai ba.
yarima yacigaba da cewa kar wanda yasaki yakawomin tashin hankali a gidana, sannan maganar kwana bayan sati guda zaku koma kowace kwana bibbiyu, jinjina kai yayi yace na fad'amuku kar inji kar ingani banason tashin hankali wlh duk wadda tanemi takawo min raini zan d'au k'wak'waran mataki a kanta, yana kaiwa nan yayi shuru na d'an lokaci sai chan yace idan akwai mai magana zata iya yi.
ba sumayya hatta ita kanta zarah taji haushin maganganunsa, sumayya ce tace yanzu dai wad'annan maganganun naka ban ganeba kafito fili kace da ni kake wannan shine adoki mutum sannan ahanasa kuka, ka gama yimin kishiya sannan ka...... hararar da yarima yawurga matane yasa tayi shuru, d'an guntun murmushi yayi yace ban miki alk'awalin bazan k'ara aureba kai koda ace a nan gaba naga wadda tayimin nakeso toh sai na aureta saidai duk wadda taji bata iya zama toh k'ofa a bud'e take dan haka kutashi kuban waje.
zarah ce tafara tashi dasauri tafita sannan sumayya.
zarah tana cikin tafiya taji muryar sumayya tace ke!
zarah batare da ta juyoba tatsaya nan sumayya tatako cike da isa tazo inda zarah take, kallonta sumayya tayi daga sama har k'asa sannan tace gimbiya zarah ko? l
dariya sumayya tayi tace gaskiya natayaki murna gaki d'iyar talakkawa ammah zaki had'a miji da gimbiya kamata, chan kuma sai gimbiya sumayya tad'aure fuska tace wlh baki isa inyi kishi da keba dan haka yazama dole kirabu da mijina, inkuma ba hakaba bakeba hatta talakkawan iyayenki sai sunsan kwad'ayi yakaisu ya baro, dan suma sai sun gane kurensu dan haka shawara ta rage ga mai shiga rijiya.
![](https://img.wattpad.com/cover/185049970-288-k834826.jpg)