*PAGE* 6⃣5⃣
Asubar fari sumayya tafarka koda daman ba wani baccin kirki bane tayi, alwallah taje tad'auro tazo tagabatar da raka'atanil fijir sannan tazauna tayi ta tasbihi da istigfari kafin atayar da sallah.
Bayan ta gama sallah alqur'ani tad'auko tashiga karanta abinda ta iya acikinsa har saida gari yai haske sannan tayi addu'a takoma takwanta ammah bacci yace d'aukarni inda kika barni, haka tayita juyi ga baccin tanaji ammah ba dama, saidai hawaye kawai da suke fita daga idanunta.
A ranar haka tawuni cikin d'akinta bata fitaba saboda kunyar iyayenta da takeji, ko breakfast batasamu tayiba koda tana jin yunwa dan rabonta da abinci tun jiya da rana.
A 6angaren memartaba ko tun dasafe yatura aje abinciko masa yarima duk inda ake tunani za'a gansa anje babushi har gidansa da yagina saida akaje ammah babu labarinsa har marece yayi ana nemansa sannan daga baya akazo aka shaida ma memartaba.
Memartaba baiji dad'iba cikin daren har so yayi yafita dakansa yak'ara bincikawa ammah su sultan ahmad suka bashi baki dak'yar sukasamu yahak'ura.
Sumayya ko sallah ce kawai take tashinta daga saman gadonta cikin d'an k'ank'anin lokaci duk tatsure tarame kamar ba itaba, chan wajen marece ummi tashigo ganin sumayya a wannan yanayin saida tatausaya mata nan tasa aka kawo mata abinci dak'yar tasamu tad'anci kad'an sannan tak'ara yi mata nasiha da wa'azi, sumayya kuka tayi sosai sannan tace ummi dan Allah kuyafemin wlh bazan k'araba, sharrin shed'anne nadaina, k'ara sautin kukanta tayi tace ummi ina jin tsoron had'uwana da ubangijina.
Ummi cike da jin tausayinta tashare mata hawayen fuskarta tace yauwa sumayya indai har kinyi tuba wadda bazaki koma abisa abinda kike aikatawa toh ubangiji zai yafe miki zai kar6i tubanki domin ubangijinmu mai tausayin bayinsane idan yaso yana yafe abinda yake tsakaninsa da bawansa komai yawan zunuban mutum Indai katuba toh zai yafe maka inyaso, hak'ine kawai baya yafewa dan wannan tsakanin mutum da wanda aka zaluntane, dan haka kicigaba da istigfari da yawan tasbihi tare da addu'a, sannan yanzu kitashi kije kinemi gafarar iyayenki dan suma suna da hak'i a gunki.
Rik'o hannun ummi tayi cikin dashashar muryarta da tasha kuka tace ummi kitaimaka min kirakani k'ila idan dakene zasu iya yafemin ammah idan naje nikad'ai korata zasuyi.
Shafa kanta ummi tayi tace kar kidamu sumayya bazasu korekiba insha Allahu, tashi muje ammah bazan shigaba kekad'ai zaki shiga.
Mik'ewa sumayya tayi dakyar take tafiya jiki babu k'wari sultana sadiya tana rik'e da ita sukanufi part d'in iyayenta.
Daga bakin k'ofa sultana taja tatsaya, nan sumayya tatura d'akin ahankali tashiga, sultan abbas zaune yake a parlournsa yana kallo ammah idan mutum yalura zai gane ba kallon yakeba dan gabad'aya hankalinsa yayi wani wajen daban, daga nesa da shi kad'an sultana sadiya ce ta buga uban tagumi ta tsura ma waje guda ido.
Shugowar sumayya yasa gabad'ayansu suka juyo suka kalleta daga nesa dasu kad'an tatsugunna bata damu da mugun kallon da sultana sadiya take watsa mataba, duk'ar da kanta tayi nan hawaye suka cigaba da zuba.
Ummah ce cikin fushi tace ubanmi kikazo yi mana nan? Ko sai kinga kin kashemu sannan hankalinki zai kwanta?
Girgiza kai tashiga yi, muryarta tana rawa tace ummah Abbah dan Allah kuyafemin wlh nadaina.
Munafukar banza wlh ko kitashi kifita kiba mutane waje ko yanzu insa6a miki.
Shuru sumayya tayi kamar ba da ita takeba saida sultana sadiya ta kwatsa mata tsawa sannan tamik'e jiki babu k'wari kallon iyayen nata tayi d'aya bayan d'aya sannan tafita tana kuka.
Ummi da take tsaye ganin ta fito tana kuka yasa tace sumayya basu hak'uraba?
'Daga mata kai sumayya tayi tace ummi kitaimaka muje tare k'ila insuka ganki zasu hak'ura.
