69

4.7K 110 0
                                    

*PAGE* 6⃣9⃣

Yarima koda sukaje 6angarensa da mamakinsa yabi ko'ina da kallo yaga angyara sosai duk anzuba masu sabbin ma'aikata da bayi, koda yaje part d'insa tsaye yatarar da guards d'insa nan suka zube suka kwashi gaisuwa, amsa musu yayi cikin sakin fuska sannan yawuce yashiga ciki komai a gyare yake fes, murmushin jin dad'i yayi dan shi kansa yasan memartaba yana sonsa sosai.

Zarah ma koda tashiga part d'inta nan kuyanginta suka kaure da murna da jin dad'in ganinta harda d'an kukansu.

Zama Zarah tayi suka gaisa cikin mutunta juna sannan tatashi tashiga bedroom d'inta ko'ina a gyare yake fes nan aka shigo mata da kayanta, saida tayi wanka tai sallah sannan tashirya nkayanta cikin watdrobe daganan tabi lafiyar gado takwanta nan bacci yai awon gaba da ita.

Sumayya ma wajen sultana bilkisu tacigaba da zama inda sultana bilkisu tacigaba da kula da ita cike da tausayinta.

Yarima bayan yagama shirinsa cikin shigarsa ta alfarma yafito a yarimansa sak fitowa yayi inda yatarar da shaheed yana jiransa saida suka k'ara gaisawa cike da jin dad'in ganin Juna sannan suka d'unguma zuwa fada.

Suna shiga nan duk mutanen da suke ciki suka zube Suna kwasar gaisuwa haka yacigaba da amsa musu cikin sakin fuska daga k'arshe da yagaji sai yakoma d'aga musu hannu ahaka suka isa har chan wajensu memartaba da waziri sai iyayensa da suke zaune, cikin girmamawa yaduk'a yagaishesu suka amsa masa sannan yaje yazauna kujerarsa da aka tanadar mashi sai kujera ta kusa da tashi shaheed yazauna.

Bayan jama'a sun nutsu memartaba lasifika yakar6a ahankali yai sallama sannan yafara yi musu godia akan addu'o'in da sukayi masa daga k'arshe yak'ara bayyanar masu da Yarima da yadawo sannan yak'ara shaida musu akan shine magajinsa ko bayan ransa.

Nan fada tarud'e da murna da kabbara cikin jin dad'i, bayan ya gama bayani yatambayi Yarima ko yana da magana nan Yarima yagirgiza kai.

Waziri ne yakar6i lasifikar yak'ara yi ma jama'a godia sannan yanuna farin cikinsa akan samun lafiyar memartaba yakuma yi murna akan bayyanar Yarima daganan yaba wasu fadawa umurni akan suje susa akawo abincin da yasa ashirya a gidansa saboda gaggarumar walima yahad'a yanaso kowa yaci yanuna farin cikinsa.

Haka akaje akazo da abincin me rai da lafiya aka zuba ma kowa na cikin fadar hatta su memartaba saida akasa masu nasu, bayan angama nan akaba kowa umurni yaci nan jama'a aka shiga ci ana jinjina ma karamcin wannan masarauta hatta su memartaba da shi kansa waziri sunci.

Shaheed ne ganin suhail baya ci yasa yata6osa yace kaci man.

Murmushi Yarima yayi yace na k'oshi, harararsa shaheed yayi yace ammah kasan bazasuji dad'iba idan sukaga bakaciba.

Jin haka yasa Yarima yad'ebo abincin cikin izza yaci, cokali biyar yayi yature abincin yajanyo wayarsa yashiga dannawa.

Bayan kowa ya gama nan sarki ya amshi lasifika yanuna godiarsa ga waziri sannan yad'auko wata alkyabba da rawani masu kyau yadamk'a ma Yarima.

Kar6a Yarima yayi cikin jindad'i sannan yanuna godiarsa, daga k'arshe yayi ma su memartaba sallama yaja shaheed suka fita, motarsa suka shiga suka nufi hospital d'insa.

Lokacin da ya isa sosai staffs d'insa suka nuna farin cikin dawowarsa, dr khalil ko rungumesa yayi cikin jin dad'i.
Yarima farin ciki yayi sosai alokacin da yaga komai yana tafiya daidai nan yanuna jin dad'insa tare da  godia ga manyan staffs d'insa.

Bayan sallar isha'i bayan ya gama shirinsa na bacci saman gadonsa yahau yakwanta kad'an kad'an ya duba lokaci yayi tsaki ganin har wajen k'arfe tara ammah zarah batazo part d'insaba, daga k'arshe mik'ewa yayi yasaka alkyabbarsa sanan yafito yanufi part d'inta.

Yarima SuhailWhere stories live. Discover now