4⃣3⃣

2.5K 295 33
                                    

Kamar an watsa min kankara ko irin nayi freezing dinnan haka na tsaya, Inata kallonta itama Tana ta kallona, ni Tsoro ne akan fuskata saboda ban taba ganin photocopy na mutum irin yadda naga fuskata a fuskarta ba, Haka na kasa dauke idanuna zuciyata se bugawa take Kamar zata balla kirjina ta fito, Ina kallo naga hawaye ya Fara gangaro mata ga kuma wani genuine smile da takeyi min shi.

"Go to her Hikmah, she's your mother, ita ta haifeki"

Haka na tsinkayi muryar Baffa yana fadamin, Juyawa nayi na kalleshi Se naga ya Gyada min kai, na kalla Mama hawaye ne taf Idanunta Tana kallona tana gyada min kai, irin hug her mana, da sauri na tafi na fada jikin matar dake tsaye. Wallahi naji wata nutsuwa da soyayya da ban taba jin irin ta ba, se kawai na fashe da kuka ina sake kankameta, a raina banda Subhanallah! Babu abinda nake maimaitawa, I was so and super excited, bayana ta dinga bubbugawa a hankali itama kukan take, munfi mintina biyar sannan na saketa amma na kankame hannunta saboda gani nake kamar guduwa zatayi, kamar Ina bude idona zanga mafarki ne da na saba yinshi a kwanakin nan. Amma dana bude I was still standing next to that woman, next to Loml💕 tana ta min Murmushi da babu Wanda ya taba min irinshi a rayuwata,

"Ni bazata zo na ganta ba, duk kin kankameta"

Wanda nake tunanin shi ne Mahaifina the CBN governor Ya fada yana hararmu, kowa a parlon seda yayi dariya, sakin hannunta nayi na nufi inda yake ban jira wani abu ba na rungumeshi, shima rungumeni yayi yana fadin

"Blessed you my child! Allah Yayi miki albarka Kinji, Daddy is sorry baby"

A hankali Wasu hawayen farin ciki suka sauka min daga idanu na, I'm so happy, ban taba jin farin cikin da nake ciki a wannan ranar ba. Seda na zauna gefen Daddy sannan Hamma Musbahu yace

"Nikam Hikmah for how long kika san Baffa da Mama ba iyayenki bane? Naga Bakiyi mamaki da akace ga real parents dinki ba"

Baffa da Alhaji suka hada bakin cewa

"Gaskiya kam Musbahu"

Hannuna Daddy ya rike, ina Murmushi nace

"Haba Hamma, ai Bazan taba canja Baffa da Mama ba, iyayena ne. Yanzun daka fadi haka se naji kunya, nake ganin Kamar ban kyauta ba. Babu Wanda ya fada min (seda na Kalli Hamma Mussadiq, Wanda ya tsura min idanun shi, nasan bazai so na fadi sunanshi ba) kawai na dade ina ayyana Baa gidanmu nake ba, naga wannan kayan sannan bana kama ban dakko halin kowa ba, to jiya birthday Dina, I was going through twitter se naga post din Daddy na missing daughter dinshi, dama na dade inajin Anya bashi bane Babana ba, so anan na tabbatar da zargina shi ne nayi maka tweeting kuma bakai retweeting ba Har na hakura"

Kowa farin ciki yake sannan Daddy yace

"Ga Grandparents dinki"

Kowanne seda ya nuna minsu, Ina binsu da hannu muna musabaha, naji dadi sosae wannan ranar seda nayi recording dinta a diary dina. Kafin wani lokaci duk su Aneeysa dasu Hamma sun taru a gidan, tamkar ana yin biki, se girke girke ake, babu Dama na mike Mama zata balla min harara Wai ina Zanje na bar Mamata.

Daga karshe dakina muka wuce nida ita, Tana ta bugawa mutane waya muna gaisawa, inajin yadda suke murna nasan nayi Saar dangi. Ina tason nace mata waye na aura amma Se naji kunyarta, se can tace min

"Azizaty, Kinada saurayi Ko? "

Wani kallo nayi mata irin saurayi kuma? Kaina na girgiza nace

"Inada aure fa"

Gyara zamanta tayi, Ina karanto disappointment din a fuskarta, Dan har seda ta runtse idanunt kafin tce

"Aure, Tun yaushe? "

Shigowar Mama yasa ban bata amsa ba, tare muka fita saboda tace mana Abinci is ready. A parlor duka muka zauna ina nanike jikinta kamar zata maidani ciki, duk inda nayi tana biye Dani da idonta, Haka dana tsaya sauraren Abu zatace

HIKMAH Where stories live. Discover now