1⃣4⃣

2.2K 257 8
                                    

*_Never employ a nanny whose house you don't know, some of them might be human traffickers_*

Dukkansu a wannan ranar suka baro Kano suka nufi maiduguri, to me yayi saura? Babu shi tunda itama Rebecca bata san inda Lulu take ba. Hafsa Tasha kuka Har seda Idanunta suka daina budewa, Aminu dake namiji ne babu kuka sede idanunshi kadai zaka kalla Kasan Tashin hankalin da yake ciki yafi na Hafsa, tunda at least nata akwai rangwami ta iya yin kuka amma shi fa? Ji yake tamkar zuciyarshi zata biyo makogaronshi ta fito Haka yake ji amma babu Hali.

Flight suka bi zuwa Maid, securities duk sun iso suna jiran isowar deputy governor da famylinshi. Yana landing motoci suka zo suka shiga motoci amma Alhaji bai saki hannun Hafsa ba even for a second, Idanunta a runtse dukda ta kasance Baka amma fuskarta ta nuna tsabar kukan da tayi.

Suna isa gida, ta nufi dakin Dada ta kwanta batareda sanin halin da take ciki ba, can kuma ta Mike ta shiga wanka sannan ta shimfida carpets ta hau sallah Don samun nutsuwa, Aikuwa Ta samu. Tana cikin karatun qurani wayarta ta Fara ringing seda ta kai aya sannan ta janyo wayar da dazun zuwansu airport ta saka SIM dinta na MTN, tana kallon number tasan Ambassador ne, she remembers kafin ta taho daga America ta bawa Zahra number, ganin kiranshi se zuciyarta ta Kara karyewa Dan tasan zatai masa abinda bazai taba so ba shi ne bazata koma America ba, auren Aminu zata koma yafi mata sauki and zuciyarta na gaya mata Aminun shi ne alkhairin kawai. Tana kallon call din Ya katse ta kasa dauka a Haka wani ya kara shigowa se lokacin Tayi ta maza ta dauka, muryar ta acan kasa suka gaisa yace

"Baa ganta ba? "

Hawaye masu dumi suka gangaro mata ta gyada kanta tareda fadin

"She's still missing, I pray wherever she's, she's safe. "

Kanshi Ya gyada da damuwa yace

"Amin Amin, kiyi mata addua Allah zai amsa. "

Itama kanta ta gyada Kamar yana tsaye sannan tace

"Kayi hakuri, dama nasha fada maka idan Allah Yayi zan aureka it will be, amma..... "

Se tayi Shiru ta kasa karasawa, jikinsa a matukar sanyaye ya mike daga Kan kujerar dining din da suke breakfast da Yaran gaba daya, bedroom dinshi Ya shige Zahra da Naeeyla suka bishi da ido jikinsu a sanyaye suma .

"Zaki koma gidan tsohon mijinki ne Haf? "

Shiru tayi har seda yace

"Ba wani abin bane ba fa Hafsa, it's normal a kada mutum a fagen soyayya amma hakan yana da kyau tsohuwar zuma ita ke nagani Haka Hausawa sukace. Ina fatan zumuncinmu zai daure har a aljanna. "

Sosae kalamansa suka taba ta amma taji dadi daya fahimce ta, Ya gane abinda take nufi, a Haka sukai sallama dukkansu kowa jiki a sanyaye, wayar ta dauka ta turawa Aminu da Alhaji text sannan ta kwanta bacci, kuma har lokacin babu Wanda ya shigo gurinta.

Lokacinda text din Hafsa ya shigo wayar Aminu yana zaune ya gama shan coffee Wanda yake sha kowanne dare kafin bacci, kwatakwata baya cikin farin ciki amma ya Zaiyi Haka Allah ya hukunta musu, coffee dinma ji yake Kamar extra daci aka kara masa, Hakanan yake sha babu yadda Zaiyi. Yana nan zaune yaji beep na wayarshi alamar shigowar text. Yasan bazai wuce Yan jaje ba hakan yasa ya share seda ya kammalla dukkan abinda yake, zuciyarshi na kwaidata masa son ganin fuskar Hafcy dinshi amma ya hakura don gani yake ba sauararenshi zatayi ba Kamar yadda takeyi kowanne lokaci.

Yana Hawa gado ya janyo wayarshi se ganin text dinta yayi, jikinshi har Bari yake wajen budewa, wani kuzari yazo mishi Yayi wani durowa daga gadon tareda kai goshinsa kasa yayi sujudus shukr yana godiya ga Allah iyakar iyawarshi, yana dago kanshi ya zaro wayar ya fito tsakar gida, Alhajin sama da Babanshi ya gani a tsaye alamar suna magana ne. Har ya juya zai koma yaji Babanshi yace

HIKMAH Where stories live. Discover now