BABI NA ASHIRIN DA HUƊU

7.5K 686 123
                                    

Kwanakin da suka biyo bayan zaman Su yakaka a gidan su doctor hamza , kwanaki ne mafiya jin daɗi da walwala agare su a bakiɗayan rayuwar su ,sun gyagije sun yi fes da su tamkar da ɗai basu taɓa shan wata wahalar rayuwa ba ,

Doctor hamza yayi bajinta sosai ta yadda ya ɗau nawin duk wasu lamuran su na yau da kullum babu gajiyawa babu ƙorafi ko tozarci irin na wasu mutanen, a gefe kuma ya gama shirin sa na sanya su a makarantu , inda ita yakaka yayi mata rajista da wata makarantar matan aure ta jeka/ka dawo boko zallah , zata fara zuwa bayan ta haihu ,

Falmata kuma yana fafutukar nema mata wata makarantar makafi mai zaman kan ta , wanda su a shekara mutane 70 kachal suke ɗauka , yana sa ran za'a samu gurbin sanya falmata , '

Amma a halin yanzu su duk biyun ya ɗauka musu wasu malamai biyu mata   ɗayar tana zuwa da rana kamar karfe sha biyu bayan ta taso daga makarantar islamiyyar da take koyarwa , sai ta zo ta koyar da su karatun addini , zuwa karfe biyun rana , wacce take koyar da su boko kuma zata iso karfe huɗu na yamma zuwa karfe shidda take tafiya , ita falmata kome da baki ake koya mata tana saurara a halin yanzu tun da ba makarantar su ta makafi aka kai ta ba , yayin da ita kuma yakaka ake koya mata har da rubutu ,

Kuma babu laifi ƙwarai suna da saurin fahimta musamman ma falmata , ba'a maimaita mata karatu , daga an fadi ta haddace sa kenan,  ga ta da baiwar harce iya fidda lafuza Sam bata da tsamin baki, "hakan ba ƙaramin farantawa doctor hamza yake ba , da alama yaran baza'a sha wahalar sauya musu rayuwa ba !

Ta ɓangaren ƙannan sa ma basu da wata matsala , zainab da hafsa sune manya kuma sun girme musu sosai zainab tana da ishirin da biyar hafsa tana da ishirin da uku ,dan haka tsakanin su da su yakaka gaisuwa ce kawai bayan haka ko kula sabgar su basa yi , basu ma cika zaman gidan ba domin a halin yanzu ma shirye shiryen bikin zainab ɗin ake nan da sati uku inda zata auri wani babban sojin sama ,

ita kuwa hafsa boko yayi zafi domin yanzu ne take matakin ƙarshe a jami'a ga kuma taya ƴar uwar ta shirye shiryen biki da suke , tunda ba uwa bace da su a kusa , kusan su biyun suke duk wasu tsare-tsaren su na ƴan mata , sai kuma ƙannen mahaifin su uku mata da su kuma suke gudanar da sauran lamuran da yakamata iyaye mata suyi ,"

dan haka daga su sai rahima da ta zama ƙawar su su duka biyun suke gudanar da lamuran su , domin ta biye musu sosai tana kwasar duk wasu gidancin su da ƙauyencin su da suke yi sumfuri-sumfuri kuma dai-dai gwargodo tana iyakar yin ta wurin wayar musu da kai a duk lokacin da suka yi wata katoɓarar .

   A halin yanzu sun samu kusan watanni biyu kenan a gidan ,

Kamar kullum bayan dawowar sa daga aikin sa da ya wuni yana yi , ya shigo bangaren sa bayan ya baro bangaren baba inda ya daɗe suna tattaunawa mafi yawa muhawarar ta su akan sha'anin auren zainab ɗin ne , suna tsare-tsaren yadda kome zai tafi cikin tsari mai kyau , sai kuma  a ƙarshe kamar koyaushe idan suka yi zama irin wannan sai hamza ya shigo da batun mahaifiyar su ko da a fakaice ne , a yau ma nema yayi da mahaifin nasu ya amince a sanyo ta cikin lamuran bikin zainab ɗin kasancewar ta babbar ɗiyar ta mace da a karon farko za'a aurar , a wannan lokacin fiye da lokutan baya ya ga bacin ran baban su , inda ya rufe ido yayi ta faɗa a ƙarshe yace kar hamza ya sake sako mahaifiyar su cikin lamuran bikin zainab , shine mahaifin su shi Allah ya ɗorawa alhakin aurar da ƴaƴan sa , ba wata chan daban ba wacce ta zaɓi rayuwar kororo akan zaman aure ,"

Idanun sa taf da hawaye ya baro sashin yana jin zuciyar sa na ƙara bunƙasa girman laifin ta ,

Kai tsaye banɗaki ya shiga yayi wanka gami da ɗauro alwalar sallar magariba da ta gabato , ya zira jallabiyar sa tare da sanya ɗan silifa ya rufe sashin nasa ya nufi cikin gidan ,"  hannun sa riƙe da wata ledar da ya biya ya ɗauko a mota mai tambarin "down town" , tare da wata bakar leda .

MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)Where stories live. Discover now