Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata ,
Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici ,
Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu ,
Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya
Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki .
Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci ,
Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta ,
Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka .
Da murmushi bisa fuskar sa yace
Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre .
Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa ,
Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar ,
Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,
Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ?
Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi ,
Sanar da ni ɗan ouwa
Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?
Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi
Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?
Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda ,
Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??
Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,
So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su !
YOU ARE READING
MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)
Non-FictionMAFARI...komai yana da farko, komai yana da tushe, komai yana da asali, HARGITSIN RAYUWA kan faru cikin ƙanƙanin lokaci. Duniyar daka saba da ita zata iya birkicewa zuwa baƙuwa a gareka cikin ƙanƙanin lokaci. Tafiya mabanbanciya da sauri a cikin ka...