BABI NA ARBA'IN DA BIYU

7.8K 891 263
                                    

Wani ɗan kuka ciki-ciki da Mama ta fara daga can cikin ɗakin kwanan su mai haɗe da nishi shi ya sa Falmata miƙewa daga inda ta durƙushe tana rishin kuka ,

A duƙe ta ƙarasa ɗakin saboda mararta da take ji ta riƙe , da taimakon hasken lantarki ta hango Mama a ƙasa ta faɗo daga kan ɗan gadon ta da yake dakin ,

Da sauri ta ƙarasa ta ɗagota tare da rungume ta a jikinta, tana tattaɓa jikin da ta ji yayi zafi rau , muryar ta na karkawa tace ,

" Mama meyasa kika faɗo daga gado ? Ina ne yake yi miki ciwo faɗa min , ? Kai ne ko ƙafar ki ko hannu ? Ko Bayan ki ne ??

Mama wacce take wani irin nishi ta riƙe hannun Falmata tare da ɗorawa akan cikinta ,ƴar muryar ta da kyar take fita tace ,

"ciki na ne ,Mama cikina yana ciwo sosai , ki bani magani zan sha ,ina so nayi bacci Mama ,

Wasu sabbin hawayen ne suka silmiyo daga gurbin idanun Falmata ,

"sannu Mama ,sannu kin ji zan baki magani yanzu ,

Bata amsa ba sai nishi da ta cigaba da yi , a hankali Falmata ta dafa cikin nata ta ji yadda ya kumbura yayi ƙem-ƙem ko numfashi da kyar take fitarwa, wani irin tausayi ne ya kamata tare da tashin hankali a lokaci guda ta nemi ciwon marar da take ji ta rasa ,

Tana dafe da cikin Mama ta fara yin addu'ar samun lafawar ciwo kowanne iri ne ,

Tashin hankalin da zuciyar ta ke ciki a lokacin yana neman kayar da ita , saboda rikicewa da jikin Mama yake neman yi da ƙarin ƙarfin nishinta ta fara ƙiran Baban ta ,

"Papa , Papa ,

Youssouf wanda shigowar sa kenan falon jikin sa a sanyaye ya zauna a kan kujera zuciyar sa cike da tashin hankali kan iƙirarin Yakaka na ya saki Falmata ko kuwa ta je ga iyayensa  , sam bai yi zaton abubuwa zasu rinchaɓe masa ya irin haka ba ,

Yasan cewa shi mai lefi ne a wajenta amma ko meyasa baza ta saurara su bi kome a sannu ba ?

Ƙiran sunan sa da Mama take yi ya sa ya miƙe ya nufi ɗakin zuciyar sa ɗauke da sabon zullumi kan tashin ciwon ta ,

A kiɗime ya ƙarasa kan su ya tsugunna ta bayan Falmata yana zagaye su duk biyun da hannuwansa da ya kai ya ɗora a cikin Mama inda ya ga Falmata ta riƙe ,

" Meye ya same ta ? Ciwon ciki take yi ,

"Papa ,

Mama ta ƙira sunan sa tana ƙokarin buɗe ido ,

" na'am princesse ina yake miki ciwo ?

'papa ciki na ka bani magani ina so na kwanta ,

"Mama ai a kwance kike , bari na kawo magani kisha kafin mu tafi hospitalisé, 

"Fatima yaushe Mama ta fara ciwon ciki ?

Ya tambaye ta yana kallon fuskarta ,

Sunkui da kai tayi tana kaucewa ganin Fuskar sa , muryar ta a ɗan dishe tace "Yanzu ne ,

Bayan ya kawo maganin ciwon ciki ya bata ta sha , ya janyeta daga jikin Falmata ya ɗora ta akan gado , " Fatima kin yi sallah kou ?

Girgiza kai tayi tana miƙewa ,

'kiyi sallah mu tai da Mama hospitalisé ,

Bata amsa ba ta ɗau hijabinta ta zura tana barin ɗakin da take jin sa a ƙuntace tunda shigowar sa ,

Ta kama hanyar da zata sada ta da ciki sashinta , sannu-sannu take tafiya tamkar wacce aka zarewa laka ,

damuwa yayi mata yawa bata taɓa zaton zuwan wannan ranar ba , saki a tsakaninta da Baban Mama ?

MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)Where stories live. Discover now