ARBA'IN DA DAYA

6.8K 957 372
                                    

Shigowar Hajja ita ta tsagaita kukan Yakaka da Falmata,

Da girmama juna suka gaisa ita da Biyamuradi Youssouf wanda ya samu da kyar ya iya harhaɗa kalmomin amsa gaisuwar Hajja , saboda jin sa da yake gaba ɗaya a birkice a gigice, tamkar babban mai laifin da yake jiran hukunci daga Alƙali , da yana da dama da tuntuni ya ɓace ɓat .

Hajja ta mayar da ganin ta gare su sai tayi saƙare tana bin su da kallon Al'ajabin yadda suka ƙaƙwume juna suna shiƙar kuka ,

" ku kuma yaran nan lafiya kuke kuwa ? Uwarɗakina Falmata ya daga zuwa sai kuka ? Ai ke yanzu kukan ki ya ƙare , farin-ciki ya kamata ki ta tayi 'yar nan , bari kuka Falmata .

Falmata ta ɗago kan ta daga jikin Yakaka idanun ta da hawaye amma tana ɗan murmushi tace ,

" Hajja ke ce wannan ?

Bata jira ta amsa mata ba ta ɗora da cigabada cewa ,

"Dole nayi kuka Hajja , wannan da take gabana yanzu ita ce Yayata da nake baki labarin ta Yakaka Mamar Mama , ta dawo ashe bata mutu ba , kukan murna nake Hajja , duk duniya a yanzu bani da wanda ya wuce ta .

Hajja ta ɗan taɓe baki , tana satar kallon Youssouf da yake wuƙi-wuƙi da ido yana shafa kan Mama da take jikin sa tana bin Yakaka da kallo ,

" aifa na ganta , labari kuma ya iske mini tun muna can , ai tare muka zo , ina gida lokacin da ta dawo daga inda tayi mafakarta tsawon shekaru ,

" Uwarɗakina lafiya ta samu ko ? , wallahi nayi murna , nayi murna Allah dai ya sakawa Babban soja da dubun Alheri , samun mijin da ya wuce shi a wannan zamanin akwai wuya , ki kama mijin ki ki riƙe ƙam-ƙam , Allah ya barku tare ya baku zuri'a masu yawa da Albarka ,

Shiru falon ya ɗauka aka rasa mai ƙarfin guiwar Amsawa ,

Ga Yakaka mummunar addu'a ta danganta addu'ar Hajja da ita dan haka tace " ba amin ba, cikin ranta tabbas ta san da Hajja take wannan kankanbar bata san wanene Youssouf bane ,

A sanyaye Youssouf ya miƙe riƙe da hannun Mama da taƙi barin jikin sa , so yake ya kaucewa sake haɗa ido da Yakaka , yana buƙatar wani ɗan saƙo da zai shiga ya rakaɓe ya haɗa kai da bango ya yi kuka ko zai ji sauƙin tashin hankalin da yake ciki , fili da baɗini bai ji daɗin dawowarta ba , bai ji daɗin bayynuwar ta ba , ya so da ta cigaba da zama a matatciyar ta tulin addu'o'in sa na riskar ta ,

Taku ɗaya yayi yana ajiye na biyu , yaji sun ƙira sunan sa a kusan tare ,

"Baban Mama ,
"Yusuf ,

Hatta hantar cikin sa sai da ta kaɗa , da jin tashin muryar ta da kaushi a ƙiran sunan sa ,

A firgice ya waigo idanun sa cikin nata da yake iya hango ƙiyayya da tsana masu ɗinbin yawa , ji yayi kamar ya durƙusa guiwa biyu ya roƙeta kadda ta fasa sirrin dake tsakanin su a yanzu .

Da sauri ya mayar da ganin sa ga Falmata wacce ya ga ta sunkuyar da kan ta yana iya hango bayyanar wani irin yanayi a tare da ita ,

"Na'am Fatima yace ,

Falmata wacce ƙiran sunan sa da Yakaka tayi ya ankarar da ita tare da tuno mata da matsayin Youssouf ɗin Na asali ga Yakaka , jikin ta yayi sanyi da tasowar wani yanayi mai suffar tsoro-tsoro daga ƙasan ranta , cikin dabarbarcewa tace ,

" un daman nace ga Maman Mama fa ? Baku gaisa ba ? Zaka fita da Mama bata gaishe da Maman ta ba ,

Da sauri ya saki hannun Mama , bai yarda ya dubi fuskar Yakaka ba , yace

" sannu dai ,

Da sassarfa ya ƙarasa barin falon Mama ta ƙara da gudu ta bi bayan sa duk ita zuwan Yakaka ya takurata ,

MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)Where stories live. Discover now