BABI NA ARBA'IN DA TARA

13.4K 987 196
                                    

MARADI-NIGER

Kwanakin da suka biyo bayan bayyanuwar mummunan aikin da Gimbiya maimounatou ta aikatawa Biyamuradi Youssouf , tare da sa hannun Mammadou da Hajiya Mama ,

Masarautar maraɗi ta kasance cikin alhini mai tarin yawa , kusan kullum aka yi zaman fada da Waziri ne ke jagoranta ba'a da wani batu da ya wuce na sake tattaunawa kan wannan mummunan lamari haɗi da yiwa Biyamuradi Addu'ar samun lafiya tare da fatan dawowar Maimartaba .

Da har yau da suke cika kwanaki ishirin da ɗaya basu baro india ba , Amma ana saka ran dawowar tasu a yau ko gobe saboda saƙon yiwuwar dawowar tasu ya iso musu .

Akwai labari daga majiya mai tushe cewar gimbiya Siyama tare da ƙanin Biyamuradi Youssouf , 'Bilal wanda shine mai binsa a haihuwa sun fara shirin tafiya India domin cigaba da jinyar sa da har kawo yau babu wanda yasan takamaimai a halin da lafiyar Youssouf ɗin ke ciki .

Ta ɓangaren Hajiya Mama kuwa duk yadda ta kai ga sanyawa idanun ta toka ta mustsiƙe ta cigaba da yin harkokin ta yadda ta saba , amma ta gagara domin yadda labarin sa hannunta da na ɗan ta wajen yunƙurin kisan da Matar Biyamuradi tayi masa , ya bazu ba a bakin bayu da hadiman cikin masarautar Maradi kaɗai ba har jama'ar gari da na wasu jahohin labari ya kai musu .

Ake kuma kucin-cina labarin tare da sake liƙa masa baƙaƙen sassa ana sake munana sa ba ƙaramin tasiri hakan yayi wajen kassara mata duk wani karsashi haɗi da ɗagawar da take tinƙaho da shi na kasancewar ta matar Sarki .

Dan haka gaba ɗaya sai take neman zama mujiya , tsarguwa take da irin kallon da bayun gidan suke mata , gefe guda ga dumuwowi birjik da suka mata ƙawanya , wanda bata saba shiga makamantan su ba , mafi girman su halin da ɗan ta tilo namiji yake ciki wanda yake tamkar ga ƙoshi ga kwana yunwa a wajen ta , domin kuwa tasan muddin Youssouf ya rasa ransa, cikin hakan akwai yiwuwar shima Mammadou ayi masa huƙunci mai tsauri da ka iya kawo ƙarshen shima tasa rayuwar .

Ga Maimartaba da bata san matsayin ta takamaimai a wajen sa ba , bayan tonon sililin da Maimounatou tayi mata a gaban sa , gefe guda kuma ga Mairamar sarki da take autar ta sannan mafi soyuwa a wajenta cikin 'ya'ya da tun bayan faruwar wannan lamarin da ta samu labarin kome bayan kuka bata wani taɓuka abun kirki ,

Rufe kanta take a ɗakin ta da yake sashin uwar-riƙon ta , ( Hajiya Umma ) ta ci kuka ,domin lamarin ya mata tsauri wajen ɗauka duka biyu a lokaci guda ,

dan kuwa bayan kasantuwar Youssouf yayan ta mafi kusanci da yawan ƙauna a tsakanin su fiye da duk sauran 'yan uwan ta , ta shaƙu da shi tunda ta buɗi ido ta ga kanta riƙe a hannuwan sa , shiga hatsarin rasa shi ba abune mai sauƙi a wajen ta ba .

Damuwar ta tana sake hauhawa da hango rugujewar zancen auren ta , tare da ma guntilewar alaƙar su ita da masoyinta da suka ɗibi tsawon shekaru uku suna soyayya wanda yake yaya ne ga gimbiya Maimounatou , uwa ɗaya uba ɗaya gaf ma ake da yanke ranar auren su cikin watannin gaba kaɗan a sha biki , sai ga shi wannan mummunan lamarin ya shata layi a tsakanin su , domin kuwa ko ba'a sanar da ita ba ta san makomar soyayyar su ita da Khaalifa , sannan tun kafin a hana ta ita ya kamata ta fara zare soyayyar sa daga ran ta , bayan abunda ƙanwar sa ta aikata ga Biyamuradi ai babu wani sauran alaƙa mai girma da zai sake shiga tsakanin masarautun nasu biyu .

Ba tun yau ba ta riga ta san wasu daga cikin munanan halayen Mahaifiyar su da ita koyaushe huɗubar ta tare da yunƙurin ta bai wuce na ganin ta raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin ta da uwar-goyon ta tare da sauran ƴan uwan ta da suka haɗa uba ɗaya ba ,

da ita kuma ko kusa bata ganin aibun su , sannan duk wasu laifuka nasu da hajiya Mama ke faɗin sun aikata ko suna kan aikatawa , ita bata kai ga kama su da ko guda ba dan haka koyaushe take biris da huɗubar ta , tare da toshe kunnuwan ta , ƙaunar ƴan uwanta a jinin ta yake tana ƙaunar su kwatankwacin ƙauna tare da zallar kulawa da su ma suke nuna mata a matsayin ta na ƙaramar ƙanwar su ,

MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)Where stories live. Discover now