Hamsin da UKU

13.4K 912 434
                                    

Tsayuwar minti ɗaya zuwa biyu tayi tana kallon ta kafin ta ƙaraso gaban gadon ta zauna ba tare da tace mata ƙala ba .

Hakan da tayi ya sake ƙular da Sofia dan haka a fusace tace " zaɓi na zo baki ko dai  yini tare da Sam ko kuwa ki fice daga gidan nan ki tafi can inda kika saba zuwa yawon ki a garin nan idan shi da ya ajiye ki ya dawo kin dawo dan yinin ki da ni a gidannan bana jin zan iya jurewa .

Yakaka wacce kan ta ke ƙasa har Sofia ta gama bayanin ta bata ce mata kome ba tamkar dai bata jin yaren da Sofia take yi ta miƙa hannu a hankali ta ɗau wayar ta ta fara dannawa ba tare da tasan me take yi ba '

Hakan da tayi ba ƙaramin tunzura Sofi tayi ba a fusace tace "Dan Ubanki watau ga mahaukaciya tana magana kin wani yi banza dan....'

Kamar an safure ta Yakaka ta miƙe daf da Sofi ta zo ta tsaya idanun ta ƙyar akan ta cikin muryar ta da bata cika ƙarfi ba tace "Duk wani cin mutumci da zage-zagen ki ya tsaya a iyakar kaina , kar domin kin ga ina yin shiru kiyi zaton za ki iya zagin iyayena na ƙyale ki .

" ban ajiye iyayena kurkusa ba idan ke kin raina naki iyayen na.....

Turo ƙofar da aka yi yasa su duk biyun waigawa .

Doctor Hamza turus yayi yana kallon su kafin ya ƙaraso fuskar sa cike da mamaki ya tattara ganin sa kan Sofi wacce har kawo lokacin bata farfaɗo ba daga ruɗanin da ta shiga kan ji da tayi Yakaka ta mayar mata da Martani har ma tana ƙoƙarin rama zagin da ta mata.

"Sofia me ya faru ? Me kika zo ...

Sai yaƙi ƙarasawa ya ɗan riƙo hannun ta ganin wani irin huci da take yi ,so yake ya jaa ta waje .

Amma sai ta ƙi da ƙarfi ta warce hannun ta kafin ta fashe da wani irin kukan baƙin-ciki .

"Na shiga ukuna Yakaka ni kike zagi ? Iyayena kike zagi Ni-ni kika zaga ? Yakaka uwata da ubana kike zagi ? Daga kawai na shigo na tayar da ku Sallah ? 

Yakaka wacce ta cika da mamaki da tsoro ta ɗago kan ta fuskar ta ɗauke da mamakin makircin Sofi da bata saba da irin sa ba tayi rau-rau da ido tana kallon Doctor Hamza wanda shi ma ita yake kallon fuskar sa a ɗaure , ta juya ga Sofia tace "ki ji tsoron Allah ni na zage ki ? Ba ke kika zage ni ba ? Ina ke ce kika shigo kawai kika fara zagi na har da Babana ?

Sofia ta zaburo zata yi magana Doctor Hamza ya dakatar da ita da cewa "saurara Sofia wai me yake damun ki ne ? Ya za ki shigowa mutane ɗaki haka da sassafe ?

Zata yi magana ya sake katse ta wannan karon muryar sa a kaurare yace "Sofia bana son tashin hankali da fitina , ran ki zai yi mummunan ɓaci muddin kika ce ...

Sofia wacce take jin zuciyar ta kamar zata fashe ganin Doctor Hamza yana shirin birkice mata kuma a gaban Yakaka .

Nan take ta haɗiye kukan kissar ta ta murje ido cikin salon ta na goggagun matan da suka raina mazajen su kunya kuma ta mata nawin ɗauka ta gatsina fuska da buɗaɗɗiyar murya tace

"Wannan wane irin rashin adalci ne kake fara rabawa a tsakanin mu tun yanzu ? Kenan dan tana ɗakin bani da ikon shigowa ɗakin ka a duk lokacin da na so ?

"Sofia ki wuce ki koma ɗakin ki kar ki ɓata min rai ki ɓata min lokaci .

Buɗe baki tayi kamar zata ce wani abu sai kuma ta fasa tana mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ita ma ita take kallo , da haƙoran ta ta cije leɓen ta na ƙasa tana yiwa Yakaka wani irin mugun kallo tayi ƙwafa kafin ta juya a fusace ta fita a ɗakin tana wani irin bugo ƙofar da har sai da Yakaka ta firgita .

Tsoron Sofi da ya ɗan yi ƙaura saboda zuciya da tayi da ta zagi Baban ta taji yana dawowa sabo fil ,ta tuno da zaɓin da tace ta bata kan ta zauna ta yini da kare a ɗaki irin na jiya ko kuma ta fita ta bar gidan to ta tafi ina ?? Yaya dacta ma ai ba zai bari ta fita ko da ƙofar gida bane kuma a can ma an mata nasiha kan fita ba mutumcin matar aure bane a dunga ganin ta a titi haka siƙau muddin ba lamarin zumunci mai ƙarfi ko aiki ko kasuwanci zata fita yi ba .

MAFARI..... (HARGITSIN RAYUWA)Where stories live. Discover now