Page 3

125 6 0
                                    

*MASOYA UKU*
_(The three lovers)_



_(True love, intense jealousy & betrayal)._



Page 3

Cike da wannan karfin guiwar Amatullah ta mik'e ta wanke fuskar ta ta saka hijjab ta fito daga d'aki, Dady ya kalle ta yace, "ina zaki je?".
"Dady zan shiga wajan Rahma ne sabida zamu je gidan Yaya Yasir tare da ita". Hamza dake zaune a yayi caraf yace, " Aunty Amatullah zan biki muje".

Mama tace, "Tashi kuje, sai kuyi ku dawo kafin malamin islamiyya yazo," cike da murna ya mik'e ta rik'e hannun sa suka fita dafa parlourn.
Suna tafe suna hira har suka k'arasa gidan sarki, da sallama ta shiga part din Umma kanta a sunkuye, a guje Humaira tazo ta d'afe ta tana fad'in, "Ga matar Yaya oyayo". Yake tayi kawai tace, " Hajiya Humaira kenan, ina Umma da Bestie?."
"Umma dai tana part din Abba ita kuma Rahma Umma ta aike ta amma yanzu zata dawo."


"Okay! To ni sauri nake zanje gidan Yaya Yasir in Umman ta fito ki gaishe ta ita kuma Bestie mayi waya da ita" ta fad'a tana k'ok'arin Barin wajan.
Ahmad da ya fito daga dakin Umma lokacin yace, "A'a kace matar Yaya ce da kanta gwara muzo mu kwashi gaisuwa ai," ya fad'a yana k'arasowa wajan cike da zolaya.


Tabe baki tayi cike da shagwab'ar da ta saba tace, "kaga ka daina bana so Allah zan hada ka da Umma." Dariya yayi yace, "Ayi hak'uri yar gatan Umma na daina, ina zuwa haka?".
"Gidan Yaya Yasir zamu je nazo mu tafi tare da Rahma Ashe Umma ta aike ta". Ahmad yace, "Muje na sauke ki to nima hanyar gidan zanyi".Tare suke fito suna hira cikin nishadi.

______________


"Finally dai Ammar zaiyi aure, ikon Allah gaskiya zanso naga wannan Amatullah din naga ta yarda akayi ta sace zuciyar aboki na haka" Khalid ya fad'a cike da tsokana.
Yasir yayi dariyar keta yace, "baka San wani Abu ba Khalid wato sai kaga gogan naka ya matse lemon tsami a kofi yana kurba yana runtse ido tsabar jaraba."

Dariya Khalid yayi sosai suka tafa da Yasir yace, "Wato mutumin anji yanayi dole a nemo lemon tsami daman ai ka girma ka rik'a kwara kayi auren tun baka fara tare yaran mutane a lungu kana lalube su ba." Dariya suka sake yi shida Yasir suka kalli Ammar dake zaune yana danna waya kamar bada shi suke ba.
Khalid ya kalli Yasir ya d'aga masa gira yace, "Yau mutumin yan miskilancin ne a kansa ya dai ka Mata ka ajjiye Wannan miskilancin sabida aure zaka yi malam." D'ago ido yayi ya kalle su ba tare da yace komai ba ya mai da kanka kan wayar dake hannun sa.


Yasir ya matso kusa dashi yace, "Ammar shirin biki ya kamata mu fara yi fa ba wai ka zauna kayi shiru muna maka magana kayi mana banza ba kamar baka ji mu ba." Yatsine fuska yayi yace "kunga ni ba wani shiri da zanyi daga an daura aure shikenan".


"Hba kai ka isa ma, ai dole ayi mana dinner ko guda d'aya ce balle ma har ball zamu had'a auren soyayya fa zakayi bana kiyayya ba malam" Yasir ya fad'a yana duban Ammar.


"Ku kadai ne kuka San auren so zanyi amma bayan Ku babu Wanda yasan da hakan dan haka zan bisu muje a a auren biyayya ne kawai."

Khalid yace, "Bafa ka isa ba dole ayi mana evens ko kad'an ne tunda mun San kana son yarinyar nan kamar ranka so why baza ka nuna farin cikin samun ta ba?."
"No Khalid ba haka bane yarinyar bata da kunya sosai ni kuma kunsan bana son rashin kunya in na nuna mata ina son bikin zata samu damar raina ni ne gwara muje a haka kawai" ya fad'a yana cize lebe.

Tsaki Khalid yayi yace, "Raini kuma na nawa? Kar ka manta yanzu auren ta zakayi kuma in ka aure ta ba zuba mata ido zaka yi ba dole ka juye mata wannan lalurar taka so ni banga abinda raini a nan ba."


Da sauri ya kalle shi yace,"What! Allah ya kiyaye ni ai ko gado d'aya banjin zan had'a da wannan yarinyar, wato ta samu damar sake Raina Ni."
Yasir da Khalid suka kalli juna suka yi murmushi sannan Yasir yace, "To kenan ba zaman aure zaku yi ba?". Mik'e zaune yayi sosai ya kalle su alamun ya gaji da magana yace, "kunfi kowa sanin dalilin da ya saka ban furta ina son ta ba sabida tayi min yarinta da yawa ina cewa ina sonta shikenan raini ya fara shiga yanzu kuma da zan aure ta kawai sai naje mata da wata bukata, kanwa ta tace fa mu dinga fadar abinda zaiyu Mana" ya fad'a yana mik'ewa daga wajan.


MASOYA UKUTempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang