Eighteen

5.7K 523 22
                                    

            Luβπα Sufyαπ

This chapter is for you guys. Ashmacute and safeenabh.

Let's see the next chappy winners.

Put a smile on my face by voting, Commenting and sharing. I love you 😍

Tun daga soron gidan su take jin hayaniyar mutane. Da mamaki tai sallama. Har kasa ta tsugunna ta gaishe dasu, suka amsa.

Mikewa tai ta kasan ido take kallon akwati nan da tasan na lefenta ne. Wani abu ne tsaye a wuyanta da ta kada hadiyewa.

Daki ta wuce. Ko hijab bata cire ba. Bata taba sanin rashin son da take ma Ado yakai haka a zuciyarta ba.

Ta dauka zata iya hakura tai biyayya wa iyayenta ta zauna da ado. Amman yau tunanin hakan kawai yasa numfashinta na wani daukewa.

Wayar dake makale kugunta ta ciro. Ta sa hannu ta shafi screen din wayar. Wasu daga cikin maganganun fuad na dawo mata.

Yakan kirata sau biyune kawai a rana. Da dare sai kuma da sassafe. Daga sun gaisa bata iya cewa komai

Saidai tai shiru tana jin yanda yake gaya mata zai dawo. Kuma zai samar musu hanyar yin rayuwa waje daya.

Sakonni kam saiya turo sunfi goma sha a rana. Haka zata bude taita kallonsu. Fin rabinsu baganewa take ba saboda da turanci yake turowa.

Kalmomin da take tsinta na turanci ba zasu shige goma ba. Inya hada da hausane kawai zata karanta.

Badai ta reply saboda bata iya ba. Inhar tace ga dalilin dayasa take daga wayar fu.ad to tayi karya.

Abu dayane take da tabbaci akai. In har ya kira saita daga. Ko tana cikin su inna ne zata shiga bandaki ta amsa wayar.

Wasu hawaye ne kebin fuskarta tana goge su. Ita kam bata son Ado ko kadan.

*

Tana nan zaune shiru taji alamun mutane na tafiya. Kamun wani lokaci gidan yayi shiru.

Tana jiyo muryar usman da inna suna magana kan lefen cewar ba karamun kokari ado yayi ba.

Akwatina ne hudu. Duk da atamfafin kanana ne sosai. Bakowa ke wannan saar ba a kauyen.

Ita kam bata wani damu da kaya ba. Addu.a take Allah ya bata karfin zuciyar daurewa ayi auren nan ko dan iyayenta.

*

Kaman kullum a kwanakin nan bakwai. Sallama taima su inna ta shige dakinta ta kwanta.

Kiran fu.ad take jira. Yau shiru bai kirata ba. Ba zatace ga adadin lokacin data dauka tana jira ba. 

Sai taji wani irin yanayi mai wahalar fassarawa. Wani daci mai bambanci dana dazun.

Juye juye kawai take baccin yaki bata hadin kai. Ta jima sosai a haka kamun wani wahalallen bacci ya dauketa mai cike da mafarkai.

*

Tun kamun asuba tai wata irin farkawa da batasan ta mecece ba. Wayar ta zaro ta duba.

Ta zuba mata idanuwa kaman fu.ad zai fito ta ciki. Kwancia tai shiru. Kan kunnenta akai kiran sallar Asuba.

Alwala tayo tai sallah. Tana idarwa ta kwashe shimfidarta ta gyara dakin.

Aikace aikacen daya kamata tayi na safe ta gama tsaf. Sannan ta koma daki ta zauna tana jiran kiran fuad dabai shigo ba.

Yinin ranar ji take kaman bata da lafiya. Kaman akwai wani bangare nata dabai cika ba. Saita samu kanta da yima fu.ad addua a duk inda yake ya kasance cikin lafiya.

Akan SoWhere stories live. Discover now