Thirty-two

6.4K 518 86
                                    

*Ina feeling kaunarku akan littafin nan #AnaTare*

Yana sauke khadee makaranta ya wuce gidansu. Tun daga yarinta shi fu.ad yake bari da goge daudar barnar da yayi.

Ba bakon abu bane wannan. Saidai rabon da maganar fu.ad ta gifta cikin gidansu ma an dauki shekaru. Momma na kokarin yi musu tun yana gidan.

Sai suyi shiru su dukansu. In abinci akeci bamai kara magana har a gama. Sai tabari. To yanzun dinma shi fu.ad ya bari da zuwa yiwa momma bayanin safiyya na nan.

Bata bar garin ba kaman yanda suke dauka. Tana nan daram kuma harda yarinya. Yar fu.ad.

*

Da sallama ya shiga gidan. Dai dai fitowar Hassan daga shi sai 3 quarter da singlet. Da fara.a ya amsa sallamar hadi da fadin.

"Yaya haneef ina kwana"

"Antashi lafiya? Babu aikine yau?"

Hassan yadan sosa kai.

"Akwai fa. Yanzun naketa shiri. Yasu anty ummie da khadee?"

Kallonshi haneef yayi sosai.

"Khadee ai tayi fushi. Tanata tambayarka"

Dariya hassan yayi.

"In shaa Allah zanje in daukota tai mana weekend."

"Allah yasa. Momma ta tashi ne?"

Dan yamutsa fuska yai kamun ya amsa da.

"Tun asuba da muka gaisa. Bansan ko ta koma bacci ba. Ka kira wayarta mana"

Kai haneef ya daga masa yana lalubo wayarshi daga aljihu. Wucewa hassan yayi abinshi.

Waje ya samu ya zauna ya kira momma a waya yace mata yana babban falo. Ko mintina biyu ba aiba ta fito.

"Ina kwana"

Haneef din ya gaishe da ita a ladabce. Saida ta karaso inda yake sannan ta amsa shi da.

"Lafiya dai ko haneef?"

Dago kai yai hadi da fadin.

"Lafiya kalau....."

Shiru yadanyi yana tunanin ta inda zai fara mata maganar kamun cikin sanyin murya yace.

"Akan fu.ad ne........."

Wani irin dokawa zuciyar momma tayi. Saboda yau kwana uku kenan bata samun wayar fu.ad din. Kuma bai kirata ba kaman yanda yakanyi.

Tanata tunanin ko lafiya. Babu dai wanda zata tunkara da maganar ne shisa tabarma ranta abin. Jin sunanshi a bakin haneef yau ba karamun tayar mata da hankali yai ba.

A kagauce tace.

"Eh meya faru?"

Ganin yanda ta tsorata yasa haneef girgiza kai da saurin fadin.

"Jiya ne lukman yazomun da wata wasiqa da take ta yawo a labarai da yanar gizo gabaki daya.

Akan wata yarinya Nana da take neman babanta. Cewar yana tunanin yarinyar yar fu.ad ce........"

Ware idanuwa momma tayi akan haneef cike da rudanin jin maganar da yake yi kamun ya ci gaba da fadin.

"Nayi kokwanto sosai ko da ya fadamun yaje makarantarsu yarinyar yaganta. Shine nai tunanin ko safiyya na garin nan.

Shine jiya da yamma bayan mun rabu da lukman din naje tsohon gidansu da fu.ad din. Momma tana nan.

Ta boye mana ne saboda bata son alaka da duk wani wanda ya hada jini da fu.ad bayan abinda ya faru.

Akan SoDonde viven las historias. Descúbrelo ahora