Twenty

5.6K 518 19
                                    

            Luβπα Sufyαπ

This chapter is for all of you. Thanks for all the voting and comments. I feel you guys.

Keep voting and commenting. Shi yake karamun karfin gwiwan ci gaba da updating.

Fu.ad ne yai kanta. Zama yai ya kamata yana jijjigawa.

"Sofi. No please. Sofi ki tashi....."

Gabaki daya ya wani gigice. Momma ce kawai ta karasa kusa dashi. Tana janyo sofi jikinta tace

"Pha.iza miko mun ruwa gashi can.... "

Jiki babu kwari pha.iza ta mikoma ta ruwan. Zubawa tadanyi a hannunta ta murza sannan ta shafa ma sofi a fuska har sau biyu.

Fu.ad kam ya tattara gabaki daya hankalin shi ya mayar kanta.

Wani dogon numfashi taja ta bude idanuwanta a firgice. Janye jikinta tai daga na momma ta matsa ta hade sa bangon.

Wani irin kuka ta saki. Karasawa fu.ad yai kusa da ita yakai hannunshi. Yanda ta janye jikinta da hanzari kaman wadda taga miciji yasa shi fasa tabata.

Muryarshi can kasa yace.

"Hey look at me. Sofi nine. Muna tare fa. Komai zaiyi dai-dai"

Kaman daga sama sukaji muryar abba yace

"Ko wani zaimun bayanin abinda ke faruwa a wajen nan? Naka sa ganewa"

Fu.ad ya dauke idanuwanshi daga kan sofi ya sauke su kan momma yana rokonta data fahimce shi.

Saidai ita tama rasa me take ji a lokacin. Mamaki? Bacin rai ko me? Gaba daya kanta ya wani daure.

Haneef dake tsaye yace.

"Kai muke jira fu.ad"

Kallon haneef yai hadi da fadin.

"Wacce kalmace baka gane ba cikin maganata ta dazun?"

Girgiza kai kawai haneef yai. Rashin kunyar ta dawo kenan. Da magana cikin gatsali da isa.

"Wacce maganar banza ce kakeyi haka fu.ad. Me ka fada da zamu gane?"

Abbah ne ke fadar hakan rai a bace.

Tausasa murya fu.ad yai.

"Ya zanyi ne abba? Daukota nai mukaje aka daura mana aure"

Karasawa inda yake abbah yai ya dauke shi da wani mari da yasa har iskar dakin ta daina watayawa na wani lokaci.

"Sake maimaitawa muji!"

Hannunshi rike da kunci yace.

"Abbah aure mukai. Wallahi ba karya nake ba"

Wani marin ya sake dauke shi dashi. Daya sa safiyya dake gefe kara rike jikinta tana kallon abba.

Nadama da kuskuren abinda sukai din na mata yawo a duk jikinta. Balle da taga abbah ya juyo da hankalinshi kanta.

Ta sake takurewa da bango kaman zata shige ciki. A fusace abba yace mata.

"Idan shi bashida hankali ina kika kai naki?  Kinsan darajar sa Allah yai miki kuwa? Kinsan halin da kika bar iyayenki ciki kika bi namiji aka daura muku aure?

Ya Rabb. Wannan wanne irin hauka ne kukayi? Kina da tabbacin zai darajaki? Zai zauna dake har abada? Zai soki fiye da yanda iyayenki suke sonki?

Wanne tabbaci kike dashi na bazai gujeki ba?......"

Da sauri fu.ad ya katse abbah da fadin.

"Wallahi zan rike ta abba. Bazan wula....... "

Momma abba ya kalla yace

Akan SoWhere stories live. Discover now