Five

5.5K 476 6
                                    

             Luβπα Sufyαπ

       

*21/02/2017*

Harya gama bubbuga kofarshi ya tafi bata bude ba. Kuka kawai takeyi. Saida tai mai isarta sannan ta tashi ta shiga toilet.

Ruwan dumi ta hada ta shiga ciki ta dan jikinta ko ina ciwo yake. Yanda nawaf ya janyota daga kan kujera ya jefar kasa.

Ba karamar buguwa tai ba. Zata iya rantsewa wani lokaci nawaf bashi da hankali.

Zaman lafiyarsu na wata biyu ne a shekaru daya da rabi da aurensu. Inhar sunan farhan ya gifta cikin gidan sai an samu matsala.

Ta rasa kalar soyayyar nan ta nawaf. Tasan da gaske yana sonta sosai. Inkuma ya daketa yana duk abinda yasan zai faranta mata.

Nawaf ya mata halacci. Ba zata manta abin daya fara mata ranar farko ba.

****

Ta dawo daga makaranta da yammaci likis. Tafiya kawai take amman da tana da wani waje da zata je da bata koma inda ya zame mata dole ta kira gida ba.

Ta jima sosai tsaye a wajen katon flat house din da yake da bala.in jan hankali daga waje.

Gidan da zaka iya rantsewa mutanen arziqi ke rayuwa a ciki. Ajiyar zuciya nuri tayi sannan ta kwankwasa kofar mai gadi ya bude mata.

Ta gaishe dashi a ladafce tsohon ya amsa cike da tausayinta a muryarshi da yanayin shi.

Tun kamun ta karasa cikin falon take jin shewa da hayaniyar maza da mata.

Duk da hakan ba bakon abu bane a wajenta bai hanata jin sabuwar tsanarshi a ranta ba.

Bata damu datai sallama ba kai tsaye ta karasa falon. Addu.a kawai take ta wuce zuwa dakinta lafiya. Bataki ace babu wanda zai kula da shigarta ba.

Kanta a kasa. Muryar Alh.baushe taji yace

"Nuriyya kin taso daga makarantar"

Bata ko nuna alamun tajishi ba. Zuciyarta sai dokawa take. Ta tsani mutumin nan da za.a bata damar kisa shine na farko dazai fado mata a rai.

Jin takunshi yasata kara sauri dan wucewa dakinta. Caraf ya rike mata hannu da duk karfinshi.

"Ke ina miki magana zaki wuce ni. Ko uwarki bata isa ta wulakantani ba balle ke banza"

Idanuwan nuriyya cike da hawaye take kokarin kwace hannunta. Amman kara janta zuwa jikinshi yake.

Kokawa ta gaske suka shiga yi. Dayake Alh.baushe ba karamin bane. Irin manyan mutanen nan ne ya riga yafi karfin nuriyya ta ko ina.

Allah ne ya bata sa.a ta gartsa masa cizo a kirji daya gigita shi. Da gudu ta nufi hanyar waje tana ihun da tasan bata da mataimaki sai Allah.

Sanin halin gidan da abinda ke faruwa yasa baba maigadi bude ma nuriyya kofa cikin hanzari dan shine kadai taimakon dazai iya yi mata.

Wani matashin saurayi ta hango tsaye jikin wata farar mota. Bandashi ko kare babu a unguwar.

Juyawa tai ta hango Alh.baushe ya fito da gudu ta karasa wajen saurayin tana wani irin kuka.

"Ke lafiyarki kuwa???"

Ya tambayeta.

Cikin kuka tace.

"Ka taimakamun wallahi zai lalatamun rayuwa"

Da mamaki a idanuwanshi yace.

"Bangane ba"

Kamun tai masa bayani Alh.baushe ya karaso inda suke yanata huci kaman mayunwacin zakin da ya kwana bai ci ba.

Ko kallon saurayin dake tsaye baiyi ba yakai hannu zai cafko nuriyya data boye bayan saurayin.

Akan SoDove le storie prendono vita. Scoprilo ora