Thirty-eight

6.1K 569 30
                                    

*Ina jin dadin yanda kuke bina a labarin nan ba tare da gajiya wa ba. Vote pls and ku fadamun ra.ayoyinku ta hanyar comments. Nagode. ILYA*

Juyawa fu.ad yai safiyya ta dakatar da shi da fadin.

"Please ka dauki mukullin motata kuje gida da Nana. Bazan iya ganinta ba yanzun......"

Ta karasa maganar muryarta na rawa. Kai ya daga mata alamar yaji ya dan kalli haneef da yake masa wani kallo dake kara karya mishi da zuciya.

Sannan ya wuce. Shi kadai yasan yanda yake jin zuciyarshi. Yakai mintina biyar tsaye riqe da handle din kofar yana maida numfashi.

Addu.a yake Allah ya bashi karfin gwiwar fuskantar nana batare da zuciyarshi ta sake karyewa ba. A hankali ya tura kofar yana jin sallamar da yake sonyi tsaye a ranshi taqi fitowa.

Idanuwanshi ya sauke kan momma. Muryarshi a dakushe yace.

"Gida zamu tafi. An sallameta"

Da fara.a momma tace.

"Alhamdulillah. Aikam nima bara na tashi......"

Kai yadan daga mata. Nazarin shi take kwata kwata a birkice yake hankalinshi kaman baya jikinshi.

"Fu.ad?"

Ta kira cike da alamun tambaya. Kallonta yai sosai yana roqonta da idanuwanshi da karta tambaye shi komai. A hankali ya girgiza mata kai.

Shiru tayi tana mikewa tace ma nana.

"To yar tsohuwa nikam zan wuce sai nazo duba ki ko?"

Dariya Nana tayi da sautinta yasa fu.ad jin zuciyarshi ta wani matse kaman zata fashe. Baya son tuna karancin lokacin dayake dashi najin wannan sautin.

"Ni zan zo ai. Mumy zata kawo ni in kwana gidanki"

Murmushi momma tai mata.

"Allah ya kawo ku lafiya. Ya kara sauqi"

Ta amsa da.

"Amin. Allah ya tsare hanya"

Momma na tafiya ta amsa ta da.

"Amin thumma amin"

Raba fu.ad tayi ta wuce batare data ce mishi komai ba. Yaji dadin hakan dan baya jin zai iya wata magana a yanda yake jin shi.

Kayan su ya fara tattarawa dan baya son ko kallon inda Nana take. Saukowa tai daga kan gadon tazo inda fu.ad ya saka warmers dinsu a babbar leda ta kamo hannunshi tana ja.

Sai da ya ja wani numfashi ya sauke shi batare daya kalle ta ba yace.

"Princess ina jinki...."

Sake jan hannun shi tayi. Bata son yanda yake kin kallonta din nan sam. Tasan me hakan yake nufi. In tun yanzun zasu fara mata irin hakan nan gaba bata san me zai faru ba.

A hankali ya juyo ya sauke idanuwanshi da suka sake launi kan fuskarta.

"Ina mumy?"

Ta tambaya tanajin komai baya mata dadi. Bata son ganinsu cikin damuwa ko kadan. Da da yanda zatai ta cire musu da tayi. Dakyar yace mata.

"Sunyi gaba dasu lukman ni dake zamu tafi"

"Hmmm"

Nana ta fadi ta saki hannunshi taje tana saka takalminta da hijab. Sannan ta dawo ta kama hannunshi suka fita tare.

Saida ya bude bayan motar ya zuba kayayyakin ciki sannan ya bude ma nana ta shiga ya zagaya shima ya shiga.

*

Akan SoWhere stories live. Discover now