Luβπα Sufyαπ
"Fu.ad yaushe ka kara lalacewa haka? Wancan mutumin bai isa ya haifeka ba har zaka iya daga hannu ka mareshi?"Anty fatima ke fadi rai a bace.
Wani numfashi yaja da alamun relief. Yace
"Thank God bashi ya haifeni ba. And karki sake dagamun hannu ba yaro bane ni"
Wani abu ya tokare mata wuya. Anty maryam tace.
"Fu.ad rashin kunya ko?"
Juyowa yai daga inda yake zaune ya watsa mata wani kallo hadi da fadin.
"Mind your own fucking business"
Fu.ad ke rashin kunyar amman lukman dake zaune shi yake jin kunya.
Gabaki daya ji yake daman motar su pha.iza ya shiga da baiga wannan bacin ran ba.
"Ka wuce muje fu.ad. And do us a favour kayi shiru muji da abu daya"
Lukman ya fadi ya juya ya kalli anty fatima dake sharar hawaye. Anty maryam kuma tayi tsuru tsuru a gefe yace.
"Dan Allah anty kuyi hakuri. Abar maganar nan. Muji da abu daya"
Kai kawai anty fatima ta daga. Fu.ad ya wani fizgi motar duk yana gwara su da jikin motar.
"Maza kashe mu to"
Lukman yace rai bace. Ko kula shi baiyi ba. Kawai tafarfasa yake a ciki.
Kaman shi anty fatima zata daga hannu ta mara akan wani tsohon daqiqin talaka.
Ya tabbata da basu hada jini ba saiya rama marinshi. Kuma sai yasa an kulle masa ita.
Suna karasawa ya samu waje yai parking. Mutane ne cike unguwar kaman zata fashe.
Anata alwala kasancewar yamma tayi sosai. Dan a hanzarta akaita makwancinta.
"Ku nemi wani ride din home"
Fu.ad ya fadi bai jira amsarsu ba ya fice ya doka murfin motar da karfi har wasu dake gefe suka juyo suka kalle shi.
"What?!!!"
Ya bukata a tsawace. Suka sadda kansu kasa. Yace yan sa idon banza kawai a ranshi.
Fitowa su anty maryam sukai sunata kuka. Dan yanzun mutuwar ke kara shigarsu da wani sabon yanayi.
Basu bi takan fu.ad ba suka wuce abinsu. Lukman yazo ya raba zai wuce shima fu.ad yace.
"Ina kuma zakaje? Aika tsayani ko?"
Cikin idanuwa lukman ya kalle shi.
"After abinda kai wallahi kunya nakeji ace tare muke"
Yana gama magana ya wuce abinshi. Wani mutum yai ma sallama suka gaisa ya karbi butar hannunshi da fu.ad ke jin ai ko wajen zai hade bazai iya wanke ko takalmi da ruwan ciki ba.
Ballantana har azo ga jikinshi. Allah kadai yasan daga inda butar ta fito da kuma kalar germs din dake jiki.
Motarshi ya bude ya dauko robar faro daya sabuwa. Ya rufe motar. Wajen ya karema kallo dan baiga inda zai tsaya yai alwala ba.
Da alamar tsantsar takura a fuskarshi ya hango wani dutse. Ya karasa wajen ya zauna ya kwance takalmin kafarshi.
Alwala yai sannan ya mayar da komai ya daure takalmin. Haneef ya hango ya karasa wajen shi.
Wani kallo haneef yai masa daga samanshi zuwa kasa.
"Ka cire wannan glass din"
Haneef yace yana dauko mukullin motarshi daga aljihu. Ya mika masa.

YOU ARE READING
Akan So
Romance"Tun daga ranar da ka shigo rayuwata komai ya dai daita" Da murmushi a fuskarshi yace "Bansan akwai abinda na rasa a tawa rayuwar ba sai da na mallake ki"