BABBAN GORO
NA
KHADEEJA CANDY
*31*
Da sauri ra nufi ɗakinta, tana shiga ta maida kofar ta rufe tana maida numfashi,
Ta daɗe a gurin a zaune, kamin ta tashi jiki ba kwari ta shiga banɗaki, ta kunna fanfo tana kwanke fuskarta da hanci. Fashewa tayi da kuka lokacin da idonta suka kai kan madubin dake gabanta ta kalli fuskarta, sai ita kanta taba kanta tausayi,a gefe ɗaya kuma Mummy take tausaya ma bata san halin da zata shiga ba idan bata raye tasan yadda Mummy take son ta kuma suka Shak'u, Mummy bata da kowa a yanzu sai ita kamar yadda itama bata da kowa sai mummu, toh idan guda ya mutu ya bar guda ya guda zaice ta rayuwarsa zata kasance?
A hankali ta sulale kasa tana tana rera kuka a hankali, ta yadda babu wanda zaiji sai wanda ke kusa da ita, jinin ko sai zubo mata yake kamar ana k'ara turo shi.
Kuka tayi sosai har idonta ya lumbura, fatar idonta tayi ja, sai da taji an kira sallah, sannan ta tashi tayi alwala ta ɗauki wani karamin tawul ta rufe hancinta dashi saboda zubar da jinin yake mata, sannan ta fito daga banɗakin kamar wanda aka cirewa lakka.
Tawul ɗin tasa ta ɗaure hancinta sannan ta canja tufafin dake jikinta ta saka hijab tayi ta soma sallar, bayan ta kare ta cire tawul ɗin ta kai shi toilet ta sake ɗauko wani tana daɗe hancin da shi kamar mai jin wari,
“Minal...-”
Jin kiran Mummy yasa ta kara gyara zaman tawul ɗin a hancinta ta juyo tana kallon kofa,
Mummy ta shigo fuskarta shimfiɗe da murmushi,
“Minal muje kici abinci nasa an... -”
Shiru tayi bata k'arasa ba lokacin da hankalin ta ya kai kan hancin Minal,
Cikin tashin hankali ta k'arasa kusa da ita, ta dafata tana tambayar ta muryar ta na rawa,
“Minal...mi..ya sa...mu hancin... Cin ki? Ko ciwon ne ya tashi”
Murmushi tayi kamar da gaske, babu abinda yake damunta,
“A'a Mummy mura ne”
Kokarin goge hancin ta tayi ta yadda Mummy ba zata gane ba, ta buɗe shi tana faɗin,
“Kin gani, mura ne babu wani abun majina ce take min zuba”
Tana faɗar hakan ta maida tawul ɗin kan hancinta, sanin idan bata mayar ba jinin zai iya mata zuba har Mummy ta gani,
Mummy bata sake ce mata komai ba sai kawai ta mata murmushi ta juya ta bar ɗakin zuciyarta na rawa da bugawa,
Sauri sauri take mai kamar gudu ta nufo falo da zimmar ɗaukar wayarta dake kan kujera,
“Lafiya Mummy?”
Kairat ta tambaya ganin yadda hankalin Mummy ya tashi,
“Minal ce na gani tana rufe hanci ina jin ciwon ta ne ya tashi tace min mura ne amman nidai ban yarda ba”
Cikin muryar kuka take bata amsar, tana neman wata number a wayarta,
Da gudu Kairat ta tashi ta nufi ɗakin Minal, durfane ta tarar da ita tana kuka kamar mai neman gafara, da sauri ta dafata idonta cikin da hawaye tace
“Sister are you crying?”
“Yes Kairat bazan iya ɓoye miki ba, but please karki faɗa ma Mummy”
“Oh my God”
Da sauri ta tashi ganin yadda jinin take zuba a hancin Minal ta nufi kofar fita,
Minal. Sai kiranta take amman bata jita ba tsabagen hankalinta baya gurin. Karo suka tashi yi da Mummy, dan tana kokarin fita Mummy ta shigo,
Da gaggauwa Mummy ta nufo Minal,
“Tashi muje asibiti na kiran Likitanki baya nan amman yace zai kira wata Dr. Zainab zata duba ki”
Tashi tayi ba musu, Mummy ta rik'a ta suka fice, gidan baya ta zauna ita da Kairat Mummy na driving suka nufi asibitin.
*** *** ***
Kaɗan-kaɗan yake cin abinci yana wasa da bakin kofin da aka zuba masa drink,
Momi na lure dashi, tun zaman shi gurin chokali huɗu kawai yakai bakinsa sai kamar wanda baya son abinci ko kuma aka sashi ci dole, Tasan matsalar iyaline take damunsa tunda Safiyyah ta faɗa masa abunda ya faru tsakanin sa da Minal, yanzu kuma yayi dawowar da ba'a zata ba kuma yaki sauka gidansa ya sauka a gurin ta,
“Saif duk kai kasa kanka cikin wannan matsalar yanzu da ace yar'uwarka ka aura zaka shiga wannan halin ne? Yaro da kai kana jama kanka matsala haka siddau”
Ajiyar zuciya ya sauke ya busar da iskar bakinsa,
“Oh Mummy so nawa zan faɗa miki Safiyyah bata daga cikin tsarin matan da nake so wallahi bazan iya aurenta ba kuma ko na aureta ba daɗi za muji ba tunda ni bana so”
“Su waɗannan da kake so ai sun nuna maka son duk cikin su babu na kwarai kowa gasa maka giɗa yake a hannu, da ita ka aura da duk haka bai faru ba tunda ita tana sonka”
“Ko tana sona dole ne sai hak'uri tunda ba ayi ma namiji auren dole”
Tashi yayi dan baya son ta kara sako masa wata maganar, ya ɗauki makulin motarsa yana faɗin
“Ga file can idan Dad yazo sai ki bashi ni zanje gida”
Taɓe baki tayi,
“Toh ka gaida gidan kuma ina son ka natsu ka sake tunani Saif.... ”
Bai ce mata komai ba ya juya ya fice ransa a jagule ita kuma ta bishi da kallon tausayin halin da ɗan nata ke ciki.
***
11pm, dai-dai Minal ta farka, ta kwashe awa biyu tana bachi, dan suna isa Dr. Zainab ta karɓe aka wuce da ita ICU Unit 2 tayi mata alurrar bachi, ta saka mata drip.
Kokarin tashi ta shiga yi sai taji an rik'a ta an tayar zaune, ɗago kai tayi suja haɗa ido ta Kairat fuskarta shakaf da hawaye,
Saurin ɗauke kai tayi, tana haɗiye yawu,
“Ki aje kukan ki har lokacin da yinsa zaiyi sai kiyi amman ba yanzu ba”
Hannayenta Kairat ta kama tana kuka,
“Minal mi yasa kika saka kanki a damuwa, Dr. Tace ciwon ki yayi tsauri sosai”
Dr. Zainab ce ta shigo, rike da wasu files, ta shiga duba Minal da tafiyar numfashinta a computer tana rubutawa.
A nan Minal tayi ta kara matse hannunta cikin na Kairat idonta cike da hawaye tace,
“Sis please promise me zaki kula da Mummy”
“I don't have to kinsan zan kula da ita, amman ki bar wannan maganar”
Hawaye ne suka shiga zuba a idon Minal, ganin hakan yasa Kairat ta kasa ɓoye kukan ta har sai da ta fasa shi,
“Please stop crying Sis you are very strong woman i wll fight it you can fight this sick”
“Bana tunanin haka Kairat wannan ba irin ciwon da kike tunani bane, blood cancer ne kuma kinsan ina da sikila. Kairat Mummy ce damuwa ta bansan irin halin da zata shiga ba. Zan mutu da bakin cikin abu biyu a rai na bakin cikin zan mutu na bar Mummy ita kaɗai kuma Saif yana min kallon maciyiyar amana”
Ido Kairat ta tsura mata tana hawaye, Dr. Zainab ma kallonta take cike da tausayawa.
KUN TUNA WACECE DR. ZAINAB?
VOUS LISEZ
BABBAN GORO
Roman d'amourNOT EDITED ⚠️ "Kayi kuskuren fahimta Saif, babu soyayyarka a cikin zuciyata ko kaɗan" Kara matsowa yayi kusa da ita, ta yadda tana iya juyo bugun zuciyarsa, yace "Ki kalli kwayar ido na ki faɗa min baki sona ki karya ta kanki da kanki indai har da g...
