BABI NA ARBA IN DA TARA

3.2K 325 24
                                        

Ji tayi kamar ana zooming ɗinta saboda tsoro. Daker ta iya rufe idonta ta furta


"Innalillahi wa innaa ilaihi raji'un"

Ta daɗe a haka kamin ta buɗe idon ta sake kallon bakin kofar, neman ta tayi ta rasa, tayi ko sama ko kasa, da sauri ta maida kofar ta rufe tana haki

Saman kujera ta dawo ta zauna dafe da zuciya,

Toh ko dai gizo idonta yake mata ne?

Shine abunda ta tambayi kanta tana lumshe, toh idan ba gizo ba kan minene tun dai Minal ba dawowa zatayi ba, wannan tsoro ne da kuma rashin sabo da zama ke kaɗai.
Tana haka taji an sake turo kofar a karo na biyu an shigo parlour, kulle idonta tayi gam, har sai da taji sallamar Saif sannan ta buɗe idon tana amsa masa

"Wa'alaikumussalam"

"Sannu da zuwa"

"Yauwa sannu dai ke kaɗai ce a gidan"

Ya faɗa yayin da yake kokarin karasawa kusa da ita, ita dai har lokacin kanta na kasa tana doubting abunda ta gani,

"Bari naje nayi wanka sai muci abinci ko?"

As usual bai tsaya jiran abunda zata ce masa ba ya nufi ɗakinsa ita ɗin bata ce masa komai ba dan abunda take tunani ya isheta. Har yayi wankan ya fito a gurin da ya bar ta ya tararda ita kuma har lokacin kanta a kasa, tsayawa yayi yana kallonta kamar maj karantar abu a fuskarta,

BABBAN GOROOnde histórias criam vida. Descubra agora