BABI NA HANSI DA TARA

5.4K 290 13
                                        


Farin hayak'i ne ya turnike gurin daga bi sani hayakin yayi sama ya fita ta windo, Saif kan kallon hayakin yake ba ko kyata ido har sai da ya daina ganinsa, sannan ya kauda kai yana jan numfashi, ya daɗe yana nazarin maganar Safiyyah da kuma ta Momy sai dai maganar Momy ce take ɓata masa rai duk lokacin daya tuna,
abunda ya aikata a yanzu gani yake ya aikata daidai ko ba komai ita ta jama kanta kuma itace silar rashin samun kwanciyar hankalin aurensa ga kuma laifinsa da Momy take gani duk a dalilinta,
koma miye ta aikata can taje ta karata tun ba shi ya aike ta ba. tsiya ke tada tsohon bashi inji Hausawa, a nan ne ya soma tunanin taya akayi Deen ya san da wannan shirin na Safiyyah? Ita tambayar da ta rika zo masa a rai kenan tana masa yawo a kwakwalwah,
wayarsa ce kawai mafita, haka wani ɓangare na zuciyarsa ya amsa masa, a hannunsa ya rik'a juya wayar bayan ya fiddo ta daga aljihu sa, kamin ya soma shafa screen ɗin yana kallon hoton lil Minal, sai da wayar da fara ringing sannan ya maida hankali akan wayar, sai dai bai kaita kunnensa ba sai har sai da mai kiran yayi daf da katsewa,

"Ta ya akayi kasan da wannan labarin?"

"Ta amsa laifinta kenan? Ka tabbatar da gake nake ko?"

Aka amsa masa daga ɗayan ɓangaren, bai damu da ba da amsar tambayar da aka masa ba sai ya a kara jaddada tasa tambayar

"Taya akayi kasan da wannan plan ɗin?"

Shima ya ɗan daɗe kamin ya amsa

"Wata rana ne na fito daga kauyen mu, sai na haɗu da motar Safiyyah ita kuma tana kunna kai cikin kauyen, ganin kamar motar dana sani yasa na juya ya rika bin motar a baya har muka raba hanya,
Ta nan ne na hango fuskar Safiyyah kasancewar glass ɗin motor a sauke yake, a haka nayi ta binsu har naga gurin da sukayi Parking, a bakin kofar gidan wani babban boka dake garin namu,

Nayi mamakin yadda akayi Safiyyah tasan da wannan bokon, tunawa da abunda tayi min ta kuma yi ma Minal sai ya kawar da wacan tunanin nawa,
Bayan naga gidan da suka sauka sai nayi tafiya sai washe gari na dawo gurin bokan na zuba masa kuɗi mai yawa, a nan dake sai ya bayyana min abunda ke tafe da ita da kuma abunda ya aikata mata, ban gasgata hakan ba har sai da naji labarin Kairat ba lafiya,
Dana je gurin Mummy dan sanar mata sai na tarar hankalinta a tashe yake bata ma saurare na balle ta fahimci me nake nufi, nasan kai kaɗai ne mafita wanda zan faɗa ko da ba zaka yarda da ni ba,
Sai dai nasan wata rana zaka gasgata ni ka kuma yarda ada abunda na faɗa"

Lumshe ido Saif yayi, lokacin da Deen ya kai aya a bayanin sa, sannan ya sauke ajiyar zuciya ya tasa leɓensa ya ce

"Thank you"

Deen bai kara ce masa komai ba ya kashe wayar,bayan kamar minti biyar wani kiran ya kara shigowa, ba tare daya duba mai kiran ba ya dannan picking yasa hands free,

"Kana ina Saif?"

Muryar Nasir ce hakan ya tabbatar masa da shine ya kira ko da ba number sa bace, ya ɗn bata lokaci kamin ya amsa

"Ina gida"

Wayar ya tsurawa ido bayan katse kiran, har lokacin zuciyarsa cike take da ɓacin rai.

Sai da Nasir ya kare masa kallo sannan ya zauna kusa dashi yana faɗin

"Lubna tace min kayi faɗa da Momy miya faru?"

Ba tare daya kalleshi ba ya amsa

"Bata faɗa maka dalilin faɗan ba bata ce maka mi nayi ba?"

"Bata ce min ba, ta dai kira ta faɗa min"

Sai a lokacin Saif ya kalleshi ya soma labarta masa abunda ya faru, dan abokin dariya ba'a ɓoye masa kuka, shiru Nasir yayi yana nazarin lamarin, bai ga. Laifin Saif ba ko kaɗan itama Momy ya san zafin rai ne ya haddasa tayi haka, kallon Saif yayi ya sake kallonsa damuwa ce kwanace a fuskarsa wanda ke nuna ta zuciya tafi wannan yawa, koba komai yasan yadda Saif ke gudun zuciyar Momy baya son ganin ɓacin ranta sam, kuma hakan kan iya haifar da ɓacin ran Abbah, Hannunsa kan kafaɗar Saif ya ce

BABBAN GORODove le storie prendono vita. Scoprilo ora