BABI NA ARBA IN DA UKU

3.5K 360 29
                                        


“Kuka kike yi ko Kairat?”

Mummy ta tambaya jin hawayen Kairat na mata zuba a bata,
   Batayi magana ba sai kawai ta kara kankanme Mummy tana cigaba da kukan, a hankali Mummy ta ɗagota ta rika fuskarta ta hannayenta tana murmushin karfin hali

“Ki daina kuka kinji ki daina mata kuka lets go home”

Ta faɗa tana kokarin saukowa saman gadon cikin da karyayyar zuciya.

     ***

Ganin yadda Saif yake kuka yasa Momi ta haɗiye nata kukan tasa hannayenta biyu ta tado da shi zaune ta rika fuskarsa ta yadd zai fuskance ta

“Kayi hakuri haka Allah ya kaddara maka haka yaso ya kasance a gareka kuka ba naka bane Saifullahi, ka zamo na miji ka yarda da kaddara mamaci baya son kuka musaman ita da ba a ko kai ta makwancintaba addu'ah ce kololuwar soyayyar da zaka nuna mata ka daina mata kuka”

Bai dai na kukan ba sai dai ya sassauta muryarsa ta yadda ita kaɗai zata iya jinsa sai Lubna dake kusa da ita,
  Wayarsa ce dake aljihu ta shi ga ringing alamar kira, bai kula wayar ba ya haɗe yawun dake bakinsa ya unkura da nufin tashi Momi tayi saurin rike shi ta zaunar ta kalli Lubna

“Dauko min ruwan sanyi”

Tashi tayi tana share hawaye ta nufi firijin, ta ɗauko mata tare da kofi ta kawo.
     Buɗewa Momi tayi ta zuba masa ruwan a kofi ta kai masa a baki. da wani irin karfi yake shan ruwa kamar wanda yayi wata bai sha ruwa ba, yana gama sha ya sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ya ɗosa kansa kan cinyar Momi ya lunshe ido.
    Hannu tasa tana shafa kanshi a hankali a zahiri tana tausayin ɗan ta ganin duk yadda ya birkice lokaci ɗaya ya koma kamar karamin yaro.

     Taɓa kofar da aka yi yasa Momi ta ɗago ta kalli Nasir da ya kunno kai cikin falon kamar marar lakka jikinsa babu kuzari, yana karasowa kusa da ita ya kai hannu ya ɗafa Saif, da sauri ya buɗe ido jajayen idanunsa ya ɗago yana kallonsa,

“I'm sorry friend”

Shine abunda Nasir ya faɗa yana matsa kafaɗar Saif hawaye na masa zuba,

“Da gaske ne ta rasu kenan!”

Saif ya tambaya idonsa taf da hawaye, kai Nasir ya ɗaga masa yana matsar kuka dake son fito masa.
  Hannu Saif ya kai ya shafa gashin kansa ya girgiza kai yana kallon zoben  Minal dake hannunshi,  bazai manta lokacin da ya karɓe zoben a hannunta ba, tana masa matsifa da faɗar

“I hate you Saif  karka cire nin zobe

Yana dariya yace

“No Minal komai zakiyi sai na ɗauki wannan zoben yayi min kyau Minal i love you”

Saif no please ni na siya abuna karka cire min ina son abuna Saif bana sonka”

“Really! Bana damuwa da rashin son da kike min ni ina sonki Minal sosai kuma yanzu ne zan nuna miki son

BABBAN GOROTempat di mana cerita hidup. Terokai sekarang