BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy
*24*
“Saif tun ɗazu ne yazo i was so sad...”
Hannu ya ɗaga mata, fuskarsa a haɗe
“Minal kin dame ni da labarin Deen bana da alaka dashi so please ki daina min a maganar sa”
ta ɗan gyara zamanta, ta fuskance shi
“Am sorry but ni yanzu yana ganin naci amanarsa fa”
Banza tayi mata kamar bai jita ba, zuwa can ya kalleta yace,
“Minal kinsan abunda nake so dake”
“A'a”
“So nake kiyi min alkawari ba zaki sake kula wani namijin ba ba zaki sake saka tufafin da zasu fitar miki da tsiraici ba, ba zaki sake kula Deen ba da duk abinda ya shafe shi”
“Saif Deen abokina ne fa”
“Ni kuma mijinki ne just promise me Baby”
Baza iya masa alkawin rabuwa da Deen ba ko kuma kin kula shi dan haka yasa ta tashi da nufin shiga cikin gidan,
“Ok i wll thing about it”
Da sauri ya riko ta yana dariya, daman yasan abune mai wahala tayi ta rabu da Deen yanzu,
“Common Minal karkice min kinfi son Deen da ni”
Dawowa tayi ta zauna,
“Saif kana da muhimmanci a gareni kana babban gurbi a zuciya matsayinka daban matsayin Deen daban bana son kana haďa matsayin sa da naka,
Saif yanzu Deen yana kallo na a matsayin mace da taci amanar ya kamata na goge wannan shatin da idonsa sukayi mani”
“Fine”
Kawai yace ya tashi, ya nufi kofar da zata fitarshi daga Garden ďin,
Da hanzari ta cigabansa,
“Haba Saif daga magana sai kayi fushi”
“Dole nayi fushi Minal nifa wadda zaki aura taya kike ganin zan iya jure kina magana da wani me kike son mutane suce ta kike son a kalleni.?”
Shiru tayi yana nazari, wani gurin yana da gaskiya sai dai ita kan bata iya rabuwa da Deen yanxu,
“Ok i wll i promise amman Saif Deen ba yanzu ba i want to talk ko him”
Kafaďunta ya dafa,
“Fine amman ba just at onces”
Kai ta ďaga masa, azuciyarta kuma ba daďi.
Hannunta yaja ta rakashi har gurin Motarsa.
****** ****** *****
“Ku ajesu a nan”
Yace da yaran da suke ďauke da akwatuna, yana nuna musu gurin da zasu aza,
Sai da suka gama jearasu tsaf sannan suka fice. Shi kuma ya xauna saman kujera yana kwalama uwar gidan kira
Da Sauri ta sauko downstairs, ďaure da tawul, jikinta kuma da sanyin ruwa, da alama wanka ta fito.
Murmushi yayi mata,
“Oh wanka kika fito ne”
“Ae dear waďannan kayan fa.?”
Ya kishingiďa da kujeara yana sauke ajiyar zuciya,
“Gasu nan dai duba ki gani”
Ba musu ta shiga buďe akwatu nan zuciyarta cike da fargaba,
Kayane na gani na faďa masu kyau da tsaďa babu abunda babu cikin tun daga kan kayan kwaliya zuwa na shafe shafe su tufafi ba a maganarsu,
Bayan ta gama dubawa ta ďago da raunanin, idanu ta kalleshi,
“Na gani Saif kayan waye.?”
“Naki ne ko baki so.?”
“Nawa fa kace?”
“Ae Momi tace na siya na kawo miki abunda babu sai ki faďa min kuma duk abinda kike so ki faďa min”
“Momi fa kace Saif ka fito kayi min magana ban gane inda ka dosa ba”
Ya ďan daďe kamin yayi mata magana dan yasan maganar ba zata mata daďi ba, ita kuma ta sakar masa ido tana mai kallon jiran amsa,
“Kayan faďan kishiya ne nan da sati biyu zanyi aure insha Allah”
Bushewa tayi da dariya, duk falon ya cika da amonta, ta nuna shi da tsaya
“Haba dai Saif bana son irin wannan wasan fa ni kasan babu abunda na tsana irin ayi min wasa lokacin da nake gaske”
Kallon, kur yayi mata,
“Ba wasa bame sweetheart wallahi da gaske nake”
Tashi tayi tsayi, fuskarta babu annuri,
“Au ashe da gaske da ake faďar kara aure zakayi ina karya tawa yau har ya rage sauran sati biyu a ďaura maka auren, kai ko kunya baka ji ka buďe baki ka faďa min har ka ďebo wannan hegun kayan ka kawo min nayi me dasu tsirara ka ganni ne amman ban ta6a sanin kai azzalumi bane sai yau Saif”
Kalamanta sun fusata shi dan shi ba irin mazan nan bane masu tsaya mata na faďa musu magana son ransu ba,
“Ke kimshin haukarki ya tsaya kanki karki kuskura faďowa kaina wallahi zaki raina kanki duk abunda zakiyi sai dai kiyi amman bazan fasa aure nan ba tunda iayayena basu hanani ba babu wadda ya isa ya hanani”
Bai jira cewarta ba ya nufi hanyar ďakinsa. Ita kuma ta shiga ďiban kayan tana zubarwa tana kuka,
“azzalumi wallahi ba za'ayi wannan auren ba mugu ni zaka ďasawa bakin ciki wallahi sai ka raina kanka”
daga nan ta zuba da gudu ďakinta, tana ihu kamar mahaukaciya.Kasan carpet ta faďi tana murje murje da kiran ta shiga uku, ta daďi a haka can wani tunani yazo mata da sauri ta nufi gurin wayarta.
YOU ARE READING
BABBAN GORO
RomanceNOT EDITED ⚠️ "Kayi kuskuren fahimta Saif, babu soyayyarka a cikin zuciyata ko kaɗan" Kara matsowa yayi kusa da ita, ta yadda tana iya juyo bugun zuciyarsa, yace "Ki kalli kwayar ido na ki faɗa min baki sona ki karya ta kanki da kanki indai har da g...
